• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwa Tsakanin Matasan Sin Da Afirka Zai Fadada Cin Gajiyar Kasashen Su

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

Bayan kammalar dandalin matasan Sin da Afirka karo na biyu da aka gudanar a ‘yan kwanakin baya ta kafar bidiyo, masana da masu fashin baki sun nuna gamsuwa da ma’anar dandalin, bisa yadda aka yi amfani da shi wajen yin kira da a karfafa kawance, da hadin gwiwa a fannoni daban daban, domin raya Sin da Afirka bisa juriya da cin moriyar juna yadda ya kamata.

Dandalin wanda kungiyar sada zumunta tsakanin jama’ar kasar Sin da ta kasashen waje ko CPAFFC ta shirya, ya hallara masu ruwa da tsaki a fannin tsara manufofi, da ma’aikatan diflomasiyya, da masana, da dalibai, da wakilai daga kungiyoyin lura da walwalar jama’a, ya jaddada muhimmancin karfafa hadin gwiwa tsakanin matasan Sin da na kasashen Afirka, a matsayin wani ginshiki na kyautata rayuwar bil adama.

  • Xi Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Ilimi Karo Na 16 Na Cibiyoyin Kimiya Na Kasashe Masu Tasowa

Wanda kuma nasarar sa za ta bude wani sabon babin goyon bayan juna tsakanin Sin da kasashen Afirka, musamman da yake batu ake yi na matasa, wadanda Bahaushe kan ce da su “Manyan Gobe”.
Alal hakika, Sin da kasashen Afirka, sun jima suna raya kawance da goyon bayan juna a lokutan yalwa da na tunkarar wahalhalu, kuma a matsayin ta na babbar kasa mai tasowa, Sin bata taba mantawa da abokan huldar ta na kasashen Afirka ba, inda take samar musu da tallafi ciki har da na kiwon lafiya, tare da taimakon samar da manyan ababen more rayuwa, kamar layukan dogo, da manyan hanyoyin mota, da gadoji, da cibiyoyin samar da lantarki, da filayen jiragen sama da sauran su.

La’akari da hakan ne ma, masana da dama ke ganin ko shakka ba bu, idan aka yi amfani da dandalin matasan Sin da Afirka, wajen yaukaka dangantakar sassan biyu, hakan zai kara ingiza cimma manyan nasarori a fannoni daban daban tsakanin sassan biyu, musamman ganin cewa, tuni an samar da manyan manufofin bunkasa hadin gwiwar sassan biyu, karkashin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka, da shawarar nan ta “Ziri Daya Da hanya Daya”.

Don haka dai, akwai bukatar matasan Sin da na kasashen Afirka su kara wucewa gaba wajen fadada kawance, da musaya, da hadin gwiwa tsakanin su, domin cimma kafuwar al’umma guda ta Sin da Afirka, mai makomar bai daya a dukkanin fannoni.

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka
Daga Birnin Sin

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Bukaci N40m Kudin Fansar Yara 20 Da Suka Sace A Neja

'Yan Bindiga Sun Sace Matafiya A Hanyar Abuja Zuwa Kogi

LABARAI MASU NASABA

Maganin Nankarwa (4)

Maganin Nankarwa (4)

November 8, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

November 8, 2025
NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

November 8, 2025
Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

November 8, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.