• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gano Dalilin Faduwar Farashin Doya A Kasuwannin Nijeriya

by Abubakar Abba
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
An Gano Dalilin Faduwar Farashin Doya A  Kasuwannin Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rahotanni sun bayyana cewa, farashin Soya ya fadi kasa war was a wasu kasuwannin da ke a jihar Neja, biyo bayan da manoman na Doyar a jihar suka fara cika kasuwannin jihar da Doyar.

Bisa binciken da aka gudanar a manyan kasuwannin da ke a jihar, musamman a kasuwar sa ke a shalkwatar Paiko da ke a cikin karamar hukumar Paikoro da kuma wanda aka gudanar a kasuwanin Gwari da Gwadabe da ke a garin Minna a cikin jihar ta Neja sun nuna cewa, farashin na Doyar ya fadi kasa war was da kusan kashi 30 a cikin dari.

  • Abin Da Ya Sa Manoman Doya A Jihar Taraba Ke Tafka Asarar Miliyoyin Naira

Daya daga cikin masu sayar da ita a kasuwar Paiko Mohammed Salihu, ya sanar da cewa, Doya kwarya 100 da ake sayar wa akan farashin naira 200,000 a baya, a yanzu ana sayar da ita daga naira 40,000 zuwa naira 70,000, inda ya ce, amma ya danganta da girman da Doyar yake da shi.

Mohammed ya ci gaba da cewa, sai dai, har yanzu akwai manomanta da ba su fara kawo ta su Doyar da suka noma zuwa kasuwanni ba, ganin cewa, a yanzu suna ci gaba da more garabasar girbin Waken Soya da suka noma a kakar noman bana ba domin suna da burin masu saye da za su sayar wa da amfanin akan sabon farashi idan farashin ta ya tashi a daga cikin watan janairun, inda hakan zai kasance dai dai da lokacin da suke shirye-shiyen sake sabon yin shukar ta.

Wasu manoman Doyar musamman wadanda suke a yankunan, Munya, Paikoro, Shiroro, Rafi da kuma na sauran wasu kananan hukumomin da ke a cikin jihar sun bayyana cewa, duk da rashin tsaron da suke fuskanta a yankunan na su, sun samu nasarar yin girbi mai yawan gaske a kakar noman ta bana.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

A wani bincike da aka gudanar ya nuna cewa, wasu manoma da suka tashi daga yankunan Shiroro, Munya, Rafi da Paikoro a lokacin daminar da tawuce saboda kalubalen rashin tsaro a yankunan, zuwa wasu yankunan da ba fuskantar kalubalen na rashin tsaron hakan ya ba su sukunin nomanta da dama, inda hakan ya sa suka samu yin girbi mai yawan gaske.

Shi ma wani mai sayen Doyar a kasuwar Gwadabe da ke a garin Minna Mohammed Musa ya tabbatar da faduwar farashin na Doyar, inda ya ce, a yanzu ya sayi Doyar babba akan naira 3,500, wacce a baya, ya sayi daga naira ar 8,000 zuwa naira 9,000.
Liman Mohammed, wani mai sayen Doyar ya ce, ya sayi Doyar kwaya takwas a ‘yan makwanin da suka shege daga naira 6,000 zuwa naira 12,000, amma a yanzu farashin ta sauka kasa matuka.

Wani mai sayen Doyar Abubakar Yahaya ya bayyana cewa, a yanzu ya sayi duk babbar Doyar duk kwaya daya a farashi daga naira 1,500 zuwa naira 2,000 wacce a baya ake sayar da duk kwaya daya babba daga farashin naira 3,000 zuwa naira 5,000.
Shi kuwa Yakubu Mustapha ya ce, farashin na Doyar ya karye ne saboda sabuwar ta da aka cike kasuwanin da ita.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanonin Duniya Na Ci Gaba Nuna Himma Da Gwazo Wajen Zuba Jari a Kasar Sin

Next Post

Sin Ta Sha Alwashin Kare Hakkokinta A Gabar Da Amurka Ta Sake Kakabawa Karin Kamfanonin Sin Takunkumi

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

2 days ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

2 days ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

2 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

2 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

3 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

3 weeks ago
Next Post
Sin Ta Sha Alwashin Kare Hakkokinta A Gabar Da Amurka Ta Sake Kakabawa Karin Kamfanonin Sin Takunkumi

Sin Ta Sha Alwashin Kare Hakkokinta A Gabar Da Amurka Ta Sake Kakabawa Karin Kamfanonin Sin Takunkumi

LABARAI MASU NASABA

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

September 7, 2025
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

September 7, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

September 7, 2025
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

September 7, 2025
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.