• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata CBN Ya Saurari Koke-koken Al’umma – Alhaji Ibrahim

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Rahotonni
0
Ya Kamata CBN Ya Saurari Koke-koken Al’umma – Alhaji Ibrahim
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gamayyar kungiyoyin matasan arewa mazauna Legas sun bayyana cewa lallai Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya saurari koke-koken al’ummar kasar nan wajen kara yawan adadin kudaden da za a dunga cirewa a duk kullum.

A baya dai, CBN ya kakaba dokar kayyade cire kudade wanda a duk kulum mutum zai iya cire naira 20,000, yayin da a mako mutum zai iya cire naira 100,000 kacal.

  • Kotu Ta Sake Hana DSS Cafke Gwamnan CBN, Godwin Emefiele
  • NIS Ta Bankado Sabbin Dabarun Da Masu Safarar Mutane Ke Amfani Da Su A Jihar Bayelsa

Sai dai daga baya CBN ya kara yawan kudaden ya tashi daga naira 100,000 zuwa naira 500,000 a duk mako. Inda kamfanoni za su iya cire naira miliyan 5 maimakon dubu dari biyar a mako. Dokar kayyade kudaden za ta fara aiki ne tun daga ranar 9 ga watan Janairun 2023.

Mafi yawancin al’ummar Nijeriya sun nuna gamsuwarsu game da wannan mataki da CBN ya dauka na kara yawan kudaden, wanda suke ganin cewa lallai CBN ya saurari koke-koken al’ummar kasar nan.

Shugaban gamayyar, Alhaji Ibrahim Galadanci ne ya bayyana hakan lokacin da yake zantawa da manema labarai.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Ya ce, “A matsayina na wadanda muke mu’amala da al’umma muna ganin sauya wannan salo da CBN ya sauya ya ji kiran talakawa. Ma’ana gwamnati ta sausauta wa marasa karfi.

“Dama mu abin da muke hange a nan shi ne, salon da CBN ya dauka kan wannan dokar kayyade kudade, ya faru ne sakamakon bata-garin ‘yan siyasa da suke wadaka da kudaden al’umma. An kakaba wannan doka ne saboda a taimaka wa al’umma, domin akwai wadanda suke sana’a a bangaren harkokin kudi da suka yi rajista da POS.

“Kamar mutumin karkara wanda ba lallai ba ne sai ya je banki. Zai iya sayar da amfanin gonarsa ya samu mai POS ya ba shi ‘yar dubu darinsa ya saka masa a asusun bankinsa.

“Tsarin da gwamnati ta bullo da shi a wannan karan, mu dai a bangarenmu gwamnati ba ta taba yin wani abu wanda muka ji dadinsa sama da wannan ba. Domin gwamnati ta fito da doka kuma ‘yan kasa suka fito suka yi ta korafi a kan gwamnati ta sassauta kuma har ta saurari koke-koken al’umma,” in ji Ibrahim Galadanci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CBNGamayyaKungiyaPOS
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’an Tsaro Sun Kuɓutar Da Wata Soja Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Iyakar Enugu Da Imo

Next Post

Bikin Nadin Sabon Sarkin Jere Na 11 Ya Kayatar

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2 weeks ago
CBN
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

3 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

3 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

4 weeks ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

4 weeks ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
Bikin Nadin Sabon Sarkin Jere Na 11 Ya Kayatar

Bikin Nadin Sabon Sarkin Jere Na 11 Ya Kayatar

LABARAI MASU NASABA

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.