• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Jam’iyyu Suka Sha Gwagwarmayar Fitar Da Mataimakan ‘Yan Takara

by Khalid Idris Doya
3 years ago
takara

Bayan kammala zabukan fitar da gwanaye na jam’iyyun siyasa musamman APC da ke mulki a Nijeriya da kuma PDP da ta yunkura take son kwace mulki a yayin babban zaben 2023 da ke tafe.

Wanda hakan ya tabbatar da Asiwaju Bola Ahmad Tinubu daga yankin Kudu a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC da kuma Atiku Abubakar daga Arewa Maso Gabas a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, sai kuma kallo ya karkata zuwa kan su waye za su zaba a matsayin mataimaka.

  • 2023: Tinubu Ya Zabi Kabir Ibrahim Masari Daga Katsina A Matsayin Mataimakinsa

Kazalika, sauran jam’iyyun irinsu NNPP ta tsayar da tsohon gwamnan jihar Kano, Rabi’u Musa Kwankwaso ne a matsayin dan takararta.

Wakilinmu ya labarto cewa manyan jam’iyyu biyun sun sha kwaranniya kan yadda za su zabi mataimaka, lamarin da ya sanya ‘yan takaran suka shiga tsaka mai wuya na neman mataimaka musamman ma a jam’iyyar APC.

A bisa lura da yadda siyasar kasar nan ke tafiya, ana duba shugaba daga wani yanki ya fito kana a zabi mataimaki daga wata yanki domin tabbatar da tafiya da kowani yanki cikin sha’anin mulki da shugabanci.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

A jam’iyyar APC dai Bola Ahmad Tinubu ya fito karara ya nuna cewa iko da dammar zabar mataimakin shugaban kasa na hannunsa ne, kan hakan ne ake kyautata zaton zai dauki dan arewa maso gabas kuma kirista. Kodayake ya sha kusa dangane da tunanin da wasu ke yi na cewa zai iya zabar musulmi kuma daga yankin arewa a matsayin mataimakinsa.

Domin neman hadin kai da cigaban jam’iyyar, masu ruwa da tsaki na APC sun yi tir da matakin daukan musulmi a matsayin mataimaki lura da cewa Bola Tinubu musulmi ne da ya zama dan takara, sun dan nace kan cewa dole ne Tinubu ya dauki kirista kuma daga yankin arewa.

A dai yau Juma’a 17 ga watan June wa’adin da hukumar zabe ta bai wa jam’iyyu na su gabatar mata da sunayen ‘yan takata da mataimakansu. Kan hakan ne suka bazama neman mataimaka.
A wata hira da aka yi da gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma, ya bayyana cewar damar zabar mataimakin shugaban kasa na hannun Tinubu ne. Ya ce, babu inda aka bayyana cikin kundin tsarin mulkin kasa cewa dole ne sai Musulmi ya dauki kirista a matsayin mataimakinsa, ya ce kawai sai ana yin hakan ne domin cigaba da kuma hadin kai a tsakanin yankunan kasar nan.

Bisa kin amincewa da wasu masu ruwa da tsaki suka yi na tikitin Musulmi da Musulmi, hakan ta sanya ake kyautata zaton Tinubu zai iya daukar tsohon Kakakin Majalisar tarayya, Honorable Yakubu Dogara a matsayin mataimakinsa.

Dogara dai kirista ne kuma ya fito ne daga yankin Arewa Maso Gabas, don haka ne ake harsashen zai iya samun wannan damar.

Kodayake bayan Dogara, akwai wasu da ake ganin Tinubu zai iya zaba kamar su Simon Lalong na jihar Filato da Nasir El-Rufa’i na Kaduna da kuma Muhammad Badaru Abubakar na Jigawa. Da kuma gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum, da kuma tsohon gwamnan Benue George Akume. Amma harsashe ya fi karfi kan Dogara dan asalin jihar Bauchi.

Kodayake daga fari Gwamnonin APC Sun so zabar wa Tinubu mataimaki, amma hakan bai samu ba, inda alamu suka nuna Tinubu da jam’iyyar APC za su yi gaban kansu ne su dubi wanda suke ganin zai iya kawo musu kuri’a da za su iya cin zabe ba tare da duba addini ko bangaren da ya fito ba.

A bangaren jam’iyyar PDP kuwa, ana kyautat zaton cewa Atiku Abubakar zai zabi gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike ne a matsayin mataimakinsa da za su yi takarar 2023 a tare.

Ana tunanin Atiku Abubakar zai zabi Wike ne domin cike kibin siyasa da kuma kasancewarsa dan yankin Kudu, lura da cewa shi Atiku ya fito daga yankin Arewa.
Wike dai ya fito neman tikitin Shugaban kasa a jam’iyyar PDP inda Atikun ya kayar da shi da kuri’u 371 yayin da shi kuma Wike din ya samu kuri’u 237 a zaben fitar da gwani da suka gudanar kwanakin baya a Abuja.

Bayan Wike akwai rade-radin cewa jam’iyyar da dan takararta Atiku Abubakar na shirin daukar tsohon gwamnan Imo Emeka Ihedioha.
Kazalika NNPP da ta tsayar da Rabi’u Musa Kwankwaso akwai yiwuwar ta dauko nata mataimakin daga Kudanci.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata
Ra'ayi Riga

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara
Labarai

Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

October 23, 2025
Next Post
‘El-Rufa’i Ya Cancanci Yabo Wajen Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba’

'El-Rufa’i Ya Cancanci Yabo Wajen Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba'

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025
Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

October 23, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kasar Sin Ta Karyata Rahoto Na Zuki-ta-malle Da Wata Cibiyar Binciken Amurka Ta Fitar Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Yammacin Afirka

October 23, 2025
An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

October 23, 2025
Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Sojoji Sun Kama Fitaccen Ɗan Bindiga Babawo Badoo Da Wasu 37 A Filato 

October 23, 2025
Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna

Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna

October 23, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.