• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Gama Aikina A Turai, Cewar Ronaldo

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Labarai
0
Ronaldo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sabon dan was an kungiyar kwallon kafa ta Al-Nassr ta kasar Saudiyya, Cristiano Ronaldo, ya bayyana cewa y agama yin duk wani abu da ya kamata yayi a kwallon kafa a nahiyar turai yanzu kuma ya koma Saudiyya domin sake sabuwar rayuwa.

Bayan kasancewar sa wanda ya fi kowanne mutum a duniya yawan magoya baya a Instagram, ya ke kuma da kimanin mabiya miliyan 158 a Facebook, tasirin Cristiano ya kara bayyana bayan komawar sa kungiyar Al-Nassr da ke Saudiyya.

  • Man U Na Shirin Yin Wuf Da Giroud Don Maye Gurbin Ronaldo

Rahotanni sun nuna cewa Ronaldo yana da magoya baya masu yawan gaske da suke binsa babu dare babu rana sama da kungiyoyin da ya buga wasa a cikinsu a tarihinsa na kwallon kafa.

Ronaldo mai shekara 37 a duniya wanda ya samu rashin jituwa da kungiyar kwallon kafa ta Manchester United, a karshe ya samu wata sabuwar kungiya a gabas ta tsakiya kuma ita ce Al-Nassr.

Gabanin neman da aka yi masa, kungiyar Al-Nassr na da magoya baya kimanin dubu 860, amma da sanarwar komawar sa kungiyar sai magoya bayanta suka karu cikin sa’o’i kalilan.
Kawo yanzu kungiyar na da magoya baya miliyan bakwai da dubu dari shida, sun karu da kusan kashi 90 cikin 100 kuma wannan ba karamar nasara bace da kungiyar ta samu.

Labarai Masu Nasaba

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar ÆŠantata

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

Ba dai wannan ne karon farko da kididdiga ta nuna yadda magoya baya ke bin Cristiano ba a kafafen sada zumunta domin lokacin da Ronaldo ya koma Jubentus a kan fam miliyan 100, kungiyar ta samu karuwar mabiya a duka kafafen sada zumunta, sa’annan Real Madrid da ya baro ta yi asarar mabiya sama da miliyan daya cikin awa 24 kamar yadda rahoton jaridar Tifo ya bayyana.
Hakan ya yi matukar tasiri inda Jubentus ta samu karuwa da kusan kashi 25 na magoya baya a duka shafukan ta na sada zumunta kungiyar ta samu sabbin mabiya miliyan shida, wanda wannan ba karamar nasara bace a gareta.

A lokacin magoya bayan sun karu zuwa miliyan 35 a Facebook, a Twitter sun kai miliyan 6.2, yayin da a Instagram suka kai miliyan 15.3 sai dai duk da cewa ana ganin kamar dan wasan na samun koma baya a kwallon kafa a zahiri, amma a shafukan sada zumunta har yanzu shi ne ke da wannan sarautar.

Irin wannan biyayyar da mabiya ke yi, suka nuna wa dan wasan lokacin da yake shirin komawa Manchester United sannan rikicin sa da kungiyar ya haifar da koma bayan mabiya gareta a kafafen sada zumunta.
Da komawar da ya yi Al-Nassr dan wasan zai rika daukar albashin dala miliyan 200 a duk shekara kuma ya zama wanda za’a fi biyan kudi a duk shekara a fagen kwallon kafa a duniya.

wadanda suka fi daukar kudi a duniya kawo yanzu akwai shi Cristiano Ronaldo wanda zai dinga daukar dalar Amurka miliyan 214 sai dan wasan PSG Kylian Mbappe mai daukar dalar Amurka miliyan 63 sai Lionel Messi mai dalar Amurka miliyan 41 sai Neymar shima yana daukar dalar Amurka miliyan 37 sannan kuma sai Andrés Iniesta mai daukar dala miliyan 31


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Zai Jagoranci Yakin Neman Zaben Tinubu A Jihohi 10

Next Post

…Ko Goyon Bayan Da Peter Obi Ke Samu Zai Yi Tasiri?

Related

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar ÆŠantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar ÆŠantata

5 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

6 hours ago
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba
Labarai

Murabus ÆŠin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin ÆŠaukar Wani Mataki

7 hours ago
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

10 hours ago
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

19 hours ago
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu
Labarai

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

21 hours ago
Next Post
Obasanjo Ya Zabi Obi A Matsayin Dan Takararsa Na Shugaban Kasa

…Ko Goyon Bayan Da Peter Obi Ke Samu Zai Yi Tasiri?

LABARAI MASU NASABA

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar ÆŠantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar ÆŠantata

June 30, 2025
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Sin Ta Kalubalanci Kasashen Yammacin Duniya Da Su Tuna Da Laifinsu Na Mulkin Mallaka

Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

June 30, 2025
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba

Murabus ÆŠin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin ÆŠaukar Wani Mataki

June 30, 2025
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

June 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.