ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Gama Aikina A Turai, Cewar Ronaldo

by Abba Ibrahim Wada
4 years ago
Ronaldo

Sabon dan was an kungiyar kwallon kafa ta Al-Nassr ta kasar Saudiyya, Cristiano Ronaldo, ya bayyana cewa y agama yin duk wani abu da ya kamata yayi a kwallon kafa a nahiyar turai yanzu kuma ya koma Saudiyya domin sake sabuwar rayuwa.

Bayan kasancewar sa wanda ya fi kowanne mutum a duniya yawan magoya baya a Instagram, ya ke kuma da kimanin mabiya miliyan 158 a Facebook, tasirin Cristiano ya kara bayyana bayan komawar sa kungiyar Al-Nassr da ke Saudiyya.

  • Man U Na Shirin Yin Wuf Da Giroud Don Maye Gurbin Ronaldo

Rahotanni sun nuna cewa Ronaldo yana da magoya baya masu yawan gaske da suke binsa babu dare babu rana sama da kungiyoyin da ya buga wasa a cikinsu a tarihinsa na kwallon kafa.

ADVERTISEMENT

Ronaldo mai shekara 37 a duniya wanda ya samu rashin jituwa da kungiyar kwallon kafa ta Manchester United, a karshe ya samu wata sabuwar kungiya a gabas ta tsakiya kuma ita ce Al-Nassr.

Gabanin neman da aka yi masa, kungiyar Al-Nassr na da magoya baya kimanin dubu 860, amma da sanarwar komawar sa kungiyar sai magoya bayanta suka karu cikin sa’o’i kalilan.
Kawo yanzu kungiyar na da magoya baya miliyan bakwai da dubu dari shida, sun karu da kusan kashi 90 cikin 100 kuma wannan ba karamar nasara bace da kungiyar ta samu.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Ba dai wannan ne karon farko da kididdiga ta nuna yadda magoya baya ke bin Cristiano ba a kafafen sada zumunta domin lokacin da Ronaldo ya koma Jubentus a kan fam miliyan 100, kungiyar ta samu karuwar mabiya a duka kafafen sada zumunta, sa’annan Real Madrid da ya baro ta yi asarar mabiya sama da miliyan daya cikin awa 24 kamar yadda rahoton jaridar Tifo ya bayyana.
Hakan ya yi matukar tasiri inda Jubentus ta samu karuwa da kusan kashi 25 na magoya baya a duka shafukan ta na sada zumunta kungiyar ta samu sabbin mabiya miliyan shida, wanda wannan ba karamar nasara bace a gareta.

A lokacin magoya bayan sun karu zuwa miliyan 35 a Facebook, a Twitter sun kai miliyan 6.2, yayin da a Instagram suka kai miliyan 15.3 sai dai duk da cewa ana ganin kamar dan wasan na samun koma baya a kwallon kafa a zahiri, amma a shafukan sada zumunta har yanzu shi ne ke da wannan sarautar.

Irin wannan biyayyar da mabiya ke yi, suka nuna wa dan wasan lokacin da yake shirin komawa Manchester United sannan rikicin sa da kungiyar ya haifar da koma bayan mabiya gareta a kafafen sada zumunta.
Da komawar da ya yi Al-Nassr dan wasan zai rika daukar albashin dala miliyan 200 a duk shekara kuma ya zama wanda za’a fi biyan kudi a duk shekara a fagen kwallon kafa a duniya.

wadanda suka fi daukar kudi a duniya kawo yanzu akwai shi Cristiano Ronaldo wanda zai dinga daukar dalar Amurka miliyan 214 sai dan wasan PSG Kylian Mbappe mai daukar dalar Amurka miliyan 63 sai Lionel Messi mai dalar Amurka miliyan 41 sai Neymar shima yana daukar dalar Amurka miliyan 37 sannan kuma sai Andrés Iniesta mai daukar dala miliyan 31

Ronaldo
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Obasanjo Ya Zabi Obi A Matsayin Dan Takararsa Na Shugaban Kasa

…Ko Goyon Bayan Da Peter Obi Ke Samu Zai Yi Tasiri?

LABARAI MASU NASABA

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.