ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Gama Aikina A Turai, Cewar Ronaldo

by Abba Ibrahim Wada
4 years ago
Ronaldo

Sabon dan was an kungiyar kwallon kafa ta Al-Nassr ta kasar Saudiyya, Cristiano Ronaldo, ya bayyana cewa y agama yin duk wani abu da ya kamata yayi a kwallon kafa a nahiyar turai yanzu kuma ya koma Saudiyya domin sake sabuwar rayuwa.

Bayan kasancewar sa wanda ya fi kowanne mutum a duniya yawan magoya baya a Instagram, ya ke kuma da kimanin mabiya miliyan 158 a Facebook, tasirin Cristiano ya kara bayyana bayan komawar sa kungiyar Al-Nassr da ke Saudiyya.

  • Man U Na Shirin Yin Wuf Da Giroud Don Maye Gurbin Ronaldo

Rahotanni sun nuna cewa Ronaldo yana da magoya baya masu yawan gaske da suke binsa babu dare babu rana sama da kungiyoyin da ya buga wasa a cikinsu a tarihinsa na kwallon kafa.

ADVERTISEMENT

Ronaldo mai shekara 37 a duniya wanda ya samu rashin jituwa da kungiyar kwallon kafa ta Manchester United, a karshe ya samu wata sabuwar kungiya a gabas ta tsakiya kuma ita ce Al-Nassr.

Gabanin neman da aka yi masa, kungiyar Al-Nassr na da magoya baya kimanin dubu 860, amma da sanarwar komawar sa kungiyar sai magoya bayanta suka karu cikin sa’o’i kalilan.
Kawo yanzu kungiyar na da magoya baya miliyan bakwai da dubu dari shida, sun karu da kusan kashi 90 cikin 100 kuma wannan ba karamar nasara bace da kungiyar ta samu.

LABARAI MASU NASABA

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ba dai wannan ne karon farko da kididdiga ta nuna yadda magoya baya ke bin Cristiano ba a kafafen sada zumunta domin lokacin da Ronaldo ya koma Jubentus a kan fam miliyan 100, kungiyar ta samu karuwar mabiya a duka kafafen sada zumunta, sa’annan Real Madrid da ya baro ta yi asarar mabiya sama da miliyan daya cikin awa 24 kamar yadda rahoton jaridar Tifo ya bayyana.
Hakan ya yi matukar tasiri inda Jubentus ta samu karuwa da kusan kashi 25 na magoya baya a duka shafukan ta na sada zumunta kungiyar ta samu sabbin mabiya miliyan shida, wanda wannan ba karamar nasara bace a gareta.

A lokacin magoya bayan sun karu zuwa miliyan 35 a Facebook, a Twitter sun kai miliyan 6.2, yayin da a Instagram suka kai miliyan 15.3 sai dai duk da cewa ana ganin kamar dan wasan na samun koma baya a kwallon kafa a zahiri, amma a shafukan sada zumunta har yanzu shi ne ke da wannan sarautar.

Irin wannan biyayyar da mabiya ke yi, suka nuna wa dan wasan lokacin da yake shirin komawa Manchester United sannan rikicin sa da kungiyar ya haifar da koma bayan mabiya gareta a kafafen sada zumunta.
Da komawar da ya yi Al-Nassr dan wasan zai rika daukar albashin dala miliyan 200 a duk shekara kuma ya zama wanda za’a fi biyan kudi a duk shekara a fagen kwallon kafa a duniya.

wadanda suka fi daukar kudi a duniya kawo yanzu akwai shi Cristiano Ronaldo wanda zai dinga daukar dalar Amurka miliyan 214 sai dan wasan PSG Kylian Mbappe mai daukar dalar Amurka miliyan 63 sai Lionel Messi mai dalar Amurka miliyan 41 sai Neymar shima yana daukar dalar Amurka miliyan 37 sannan kuma sai Andrés Iniesta mai daukar dala miliyan 31

Ronaldo
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Obasanjo Ya Zabi Obi A Matsayin Dan Takararsa Na Shugaban Kasa

…Ko Goyon Bayan Da Peter Obi Ke Samu Zai Yi Tasiri?

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.