• English
  • Business News
Monday, June 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asalin Abin Da Ya Faru Tsakanin Abba Gida-gida Da Uwargidan Shugaban DSS

by Bello Hamza and Abdullahi Muh'd Sheka
2 years ago
in Rahotonni
0
Asalin Abin Da Ya Faru Tsakanin Abba Gida-gida Da Uwargidan Shugaban DSS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

A makon jiya ne aka samu wata takaddama a tsakanin dan takarar gwamnan Jihar Kano a karkashin jam’iyyar NNPP, Abba Kabir Yusuf wanda aka fi sani da Abba Gida-gida da Uwargidar shugaban Hukumar DSS Aisha Yusuf Bichi a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano a yayin da magoya bayan mutanen biyu suka tayar da jijiyar wuya a tsakanin su har ta kai ga furuce-furuce a kafafen sadarwa na zamani, Wakilanmu sun bi diddigi don gano asalin abin da ya faru da kuma yadda abin ya nemi ya tunbatsa har ya kusan daukar sabon salo.

Matar babban daraktan tsaro na farin Kaya na kasa (DSS) ta sa an tsare dan takarar kujerar Gwamnan Kano na Jam’iyyar NNPP na Kano Injiniya Abba Kabir Yusif Wanda a kafi sani da (Abba Gida-gida) tare da bada umarnin lakadawa hadiminsa duka a filin sauka da tashin jirgen sama a Malam Aminu Kano.

  • Turkashi: Aisha Bichi Ta Ce Jami’an Tsaron Farin Kaya Su Kamo Mata Abba Gida-Gida

Kamar yadda rahotanni suka nuna mai dakin babban Darakta hukumar jami’an tsaro na farin kaya (DSS), Aisha Yusuf Bichi, ta bada umarnin a tsare dan takarar Gwamnan na jam’iyyar NNPP a Kano, Abba Kabir Yusuf, inda ta hana shi hawa jirgi da ga Kano zuwa Abuja.
Dambarwar ta faru ne a kofar shiga bangaren matafiya masu ido da Kwalli (alfarma) na filin sauka da tashin jirgen sama na Malam Aminu Kano, yayin da ayarin motocin Abba Kabir Yusuf, wanda a ka fi sani da Abba Gida-gida, su ka haifar da cinkoso a lokacin da ita uwargidan Gidan babban Daraktan Hukumar tsaron farin kayan ke Kan hanyarta ta shiga filin Jirgin.
Lamarin da ya haifar wa da ayarin motocin da ke tare a taron Aisha Bichi tsaiko, yayin da ta ke shiga bangaren masu ido da kwallin domin tashi zuwa Abuja.
Wannan cunkoso da motocin wancan dan takara ya haifar ne ya fusata Aisha Bichi, inda dogarawanta su ka rika duka kan mai uwa da wabi da ababen hawa saboda raina Hajiya da suke zargin tawagar wancan dan takara ya yi.
Shaidun gani da ido sun ce da kurar ta lafa, sai shi Injiniya Abba Abba Kabir Yusif (Abba Gida-gida) ya je don ya yi mata korafin abinda dogaranta su ka yi, a matsayin ta na kawar mai dakinsa, inda ta nuna matukar bacin ranta, har ta ke cewa ba za ta bari ya zama Gwamna a Kano ba.
Daga nan dai, in ji majiyoyi, sai ga karin jami’an tsaron farin kaya sun zo, inda su ka tsare Abba Gida-gida har sai da Aisha Bichi ta shiga jirgi ta tashi zuwa Abuja.
Wasu majiyoyin ma sun ce kafin ta tashi zuwa Abuja, a lokacin da ta ke ta fada, Aisha Bichi ta hango wani hadimin Abba Gida-gida, Garba Kilo yana daukar ta a waya, inda ta sa dogaran ta su “Harbe shi kuma ba abin da za a yi.” a cewar majiyar data nemi a sakaya sunanta.
Uwar Gidan babban Daraktan Hukumar tsaron farin kayan ta ci gaba da fada, ta kuma rantse cewa Abba Gida-gida ba zai shiga jirgi daya da ita ba. Haka dai aka ci gaba da tsare Abba har sai da jirgin ya tashi da matar Daraktan,” in ji majiyar.
Lamarin ya faru ranar Lahadin data gabata, amma kuma wata majiya da bamu tabbatar da sahihancinta ta rawaito cewa, Uwargidan Daraktan Hukumar tsaron farin kayan ta je har gida inda ta baiwa shi Abba Kabir Yusif hakuri bayan jan kunenta da maigidanta ya yi tare da umartarta take ta bashi hakuri.
Alhaji Abba Gwale shima ya yi tsokaci Kan wannan sabata juyetan da ke kara haska wani lamari da ke bukatar yi wa kallon tsanaki, inda ya bayyana cewa, Duk Nijeriya mutane 15 doka ta sahalewa yin amfani da jiniya (Amsa Kuwwa). A ciki babu shugaban jami’an tsaro na farin kaya ballantana matar sa, kuma hukuncin yin amfani da jiniya ga wanda doka bata amince masa ba.
A wani bangare kuma, Shugaban hukumar DSS Yusuf Magaji Bichi, ya bayyana cewa, ya bayyana cewa, ya gano wani shiri na musamman da wasu suka nyi don bata masa suna dana iyalansa, wannan kuma yana faruwa ne saboda mastayarsa ba kan wasu kururin gwamnati da kuma yadda yake gabatar da aikinsa ba tare da tsoro ba.
Ya ce wadannan mutane sun shirya amfani da kungiyoyi masu zaman kansu wajen shirya zanga-zanga da taruka inda za su yi kokarin bata masa suna dana iyalansa.
Yusuf Bichi ya na magana ne a takardar sanarwa da mai magana da yawujn hukumar DSS, Peter Afunanya ya sanya wa hannun aka kuma raba wa manema labarai a Abuja. Ya kuma tabbatar da faruwar takaddama a tsakanin matar Yusuf Bichi da dan takarar gwamnan Jihar kano na jami’iyyar NNPP a filin jigin saman a Malam Aminu Kano inda jami’an DSS da ke rakiyar Aisha Bich suka dakatar da Abba Gida-gida shiga jirgin saman, suna mayar da martani ne bayan da motocin da ke cikin tawagar Abba Gida-gida suka tare hanya abin da ya jawo wa Aisha Bichi jinkiri ita da jama’ar ta.
Sanarwa ta kara da cewa, “Hukumar DSS ba za ta zura ido tana kallon wasu gungun jama’a suna furucin raini ga shugaban da ma’aiakatan hukumar ba saboda wata mastalar da suke fuskanta, kuna kuma kira ga al’umma da su yi watsi da duk wata farfaganda na batanci da za a yi na bata sunan shugaban hukumar.
“Muna kuma kara jaddada goyon bayanmu ga shugaban kasa za kuma mu ci gaba da fuskantar duk wata barazana da ke nemi kawo cikas ga zaman lafiyar kasar nan musamman zaben da ke tafe a cikin wannan shekarar.” In ji sanarwar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Next Post

Boko Haram Damfara Ce Da Aka Shirya Don Tarwatsa Nijeriya Kawai -Buhari

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

1 week ago
Abba Gida-gida
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

2 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

3 weeks ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

3 weeks ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
Boko Haram Damfara Ce Da Aka Shirya Don Tarwatsa Nijeriya Kawai -Buhari

Boko Haram Damfara Ce Da Aka Shirya Don Tarwatsa Nijeriya Kawai -Buhari

LABARAI MASU NASABA

Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

June 23, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Yakin Iran Da Isra’ila Ya Haifar Da Tashin Farashin Litar Man Fetur A Nijeriya

June 23, 2025
Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

June 23, 2025
Gwamnan Abba Kabir Yusuf tare da Arch. Ali Hassan

Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan

June 23, 2025
2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

June 22, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

June 22, 2025
Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

June 22, 2025
Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

June 22, 2025
Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

June 22, 2025
Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

June 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.