• English
  • Business News
Tuesday, August 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asalin Abin Da Ya Faru Tsakanin Abba Gida-gida Da Uwargidan Shugaban DSS

by Bello Hamza and Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
in Rahotonni
0
Asalin Abin Da Ya Faru Tsakanin Abba Gida-gida Da Uwargidan Shugaban DSS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

A makon jiya ne aka samu wata takaddama a tsakanin dan takarar gwamnan Jihar Kano a karkashin jam’iyyar NNPP, Abba Kabir Yusuf wanda aka fi sani da Abba Gida-gida da Uwargidar shugaban Hukumar DSS Aisha Yusuf Bichi a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano a yayin da magoya bayan mutanen biyu suka tayar da jijiyar wuya a tsakanin su har ta kai ga furuce-furuce a kafafen sadarwa na zamani, Wakilanmu sun bi diddigi don gano asalin abin da ya faru da kuma yadda abin ya nemi ya tunbatsa har ya kusan daukar sabon salo.

Matar babban daraktan tsaro na farin Kaya na kasa (DSS) ta sa an tsare dan takarar kujerar Gwamnan Kano na Jam’iyyar NNPP na Kano Injiniya Abba Kabir Yusif Wanda a kafi sani da (Abba Gida-gida) tare da bada umarnin lakadawa hadiminsa duka a filin sauka da tashin jirgen sama a Malam Aminu Kano.

  • Turkashi: Aisha Bichi Ta Ce Jami’an Tsaron Farin Kaya Su Kamo Mata Abba Gida-Gida

Kamar yadda rahotanni suka nuna mai dakin babban Darakta hukumar jami’an tsaro na farin kaya (DSS), Aisha Yusuf Bichi, ta bada umarnin a tsare dan takarar Gwamnan na jam’iyyar NNPP a Kano, Abba Kabir Yusuf, inda ta hana shi hawa jirgi da ga Kano zuwa Abuja.
Dambarwar ta faru ne a kofar shiga bangaren matafiya masu ido da Kwalli (alfarma) na filin sauka da tashin jirgen sama na Malam Aminu Kano, yayin da ayarin motocin Abba Kabir Yusuf, wanda a ka fi sani da Abba Gida-gida, su ka haifar da cinkoso a lokacin da ita uwargidan Gidan babban Daraktan Hukumar tsaron farin kayan ke Kan hanyarta ta shiga filin Jirgin.
Lamarin da ya haifar wa da ayarin motocin da ke tare a taron Aisha Bichi tsaiko, yayin da ta ke shiga bangaren masu ido da kwallin domin tashi zuwa Abuja.
Wannan cunkoso da motocin wancan dan takara ya haifar ne ya fusata Aisha Bichi, inda dogarawanta su ka rika duka kan mai uwa da wabi da ababen hawa saboda raina Hajiya da suke zargin tawagar wancan dan takara ya yi.
Shaidun gani da ido sun ce da kurar ta lafa, sai shi Injiniya Abba Abba Kabir Yusif (Abba Gida-gida) ya je don ya yi mata korafin abinda dogaranta su ka yi, a matsayin ta na kawar mai dakinsa, inda ta nuna matukar bacin ranta, har ta ke cewa ba za ta bari ya zama Gwamna a Kano ba.
Daga nan dai, in ji majiyoyi, sai ga karin jami’an tsaron farin kaya sun zo, inda su ka tsare Abba Gida-gida har sai da Aisha Bichi ta shiga jirgi ta tashi zuwa Abuja.
Wasu majiyoyin ma sun ce kafin ta tashi zuwa Abuja, a lokacin da ta ke ta fada, Aisha Bichi ta hango wani hadimin Abba Gida-gida, Garba Kilo yana daukar ta a waya, inda ta sa dogaran ta su “Harbe shi kuma ba abin da za a yi.” a cewar majiyar data nemi a sakaya sunanta.
Uwar Gidan babban Daraktan Hukumar tsaron farin kayan ta ci gaba da fada, ta kuma rantse cewa Abba Gida-gida ba zai shiga jirgi daya da ita ba. Haka dai aka ci gaba da tsare Abba har sai da jirgin ya tashi da matar Daraktan,” in ji majiyar.
Lamarin ya faru ranar Lahadin data gabata, amma kuma wata majiya da bamu tabbatar da sahihancinta ta rawaito cewa, Uwargidan Daraktan Hukumar tsaron farin kayan ta je har gida inda ta baiwa shi Abba Kabir Yusif hakuri bayan jan kunenta da maigidanta ya yi tare da umartarta take ta bashi hakuri.
Alhaji Abba Gwale shima ya yi tsokaci Kan wannan sabata juyetan da ke kara haska wani lamari da ke bukatar yi wa kallon tsanaki, inda ya bayyana cewa, Duk Nijeriya mutane 15 doka ta sahalewa yin amfani da jiniya (Amsa Kuwwa). A ciki babu shugaban jami’an tsaro na farin kaya ballantana matar sa, kuma hukuncin yin amfani da jiniya ga wanda doka bata amince masa ba.
A wani bangare kuma, Shugaban hukumar DSS Yusuf Magaji Bichi, ya bayyana cewa, ya bayyana cewa, ya gano wani shiri na musamman da wasu suka nyi don bata masa suna dana iyalansa, wannan kuma yana faruwa ne saboda mastayarsa ba kan wasu kururin gwamnati da kuma yadda yake gabatar da aikinsa ba tare da tsoro ba.
Ya ce wadannan mutane sun shirya amfani da kungiyoyi masu zaman kansu wajen shirya zanga-zanga da taruka inda za su yi kokarin bata masa suna dana iyalansa.
Yusuf Bichi ya na magana ne a takardar sanarwa da mai magana da yawujn hukumar DSS, Peter Afunanya ya sanya wa hannun aka kuma raba wa manema labarai a Abuja. Ya kuma tabbatar da faruwar takaddama a tsakanin matar Yusuf Bichi da dan takarar gwamnan Jihar kano na jami’iyyar NNPP a filin jigin saman a Malam Aminu Kano inda jami’an DSS da ke rakiyar Aisha Bich suka dakatar da Abba Gida-gida shiga jirgin saman, suna mayar da martani ne bayan da motocin da ke cikin tawagar Abba Gida-gida suka tare hanya abin da ya jawo wa Aisha Bichi jinkiri ita da jama’ar ta.
Sanarwa ta kara da cewa, “Hukumar DSS ba za ta zura ido tana kallon wasu gungun jama’a suna furucin raini ga shugaban da ma’aiakatan hukumar ba saboda wata mastalar da suke fuskanta, kuna kuma kira ga al’umma da su yi watsi da duk wata farfaganda na batanci da za a yi na bata sunan shugaban hukumar.
“Muna kuma kara jaddada goyon bayanmu ga shugaban kasa za kuma mu ci gaba da fuskantar duk wata barazana da ke nemi kawo cikas ga zaman lafiyar kasar nan musamman zaben da ke tafe a cikin wannan shekarar.” In ji sanarwar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Next Post

Boko Haram Damfara Ce Da Aka Shirya Don Tarwatsa Nijeriya Kawai -Buhari

Related

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

2 weeks ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

2 weeks ago
Fyade
Rahotonni

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

3 weeks ago
APC
Manyan Labarai

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

3 weeks ago
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari
Labarai

Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

4 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

4 weeks ago
Next Post
Boko Haram Damfara Ce Da Aka Shirya Don Tarwatsa Nijeriya Kawai -Buhari

Boko Haram Damfara Ce Da Aka Shirya Don Tarwatsa Nijeriya Kawai -Buhari

LABARAI MASU NASABA

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

August 11, 2025
Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

August 11, 2025
An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

August 11, 2025
Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

August 11, 2025
Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

August 11, 2025
Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

August 11, 2025
Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

August 11, 2025
Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

August 11, 2025
Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

August 11, 2025
Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

August 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.