ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Turkashi: Aisha Bichi Ta Ce Jami’an Tsaron Farin Kaya Su Kamo Mata Abba Gida-Gida

by Sulaiman
3 years ago
Abba Gida-gida

Matar shugaban SSS ta umarci jami’ai su kama Abba Kabir, kuma su hallaka guda cikin hadimansa.

 

Aisha Bichi, wacce mata ce ga shugaban hukumar tsaron farin kaya (SSS), Yusuf Bichi, tayi umarnin a kama dan takarar gwamnan Kano na jam’iyyar NNPP, Abba Kabir Yusuf (Abba Gida Gida) domin hana shi hawa jirgin Max Air daga Kano zuwa Abuja a daren ranar Lahadi, sakamakon tsaiko da tawagar Abba ta janyo a filin sauka da jiragen sama na Malam Aminu Kano dake Kano.

ADVERTISEMENT
  • Abba Gida-Gida Ya Maka Shugaban APC Na Kano A Kotu Kan Kalaman Tunzura Mutane

Wani Rahoto da jaridar Daily Nigerian ta fitar, ya bayyana cewa, tsaikon ya bata ran ita Aisha, lamarin da yasa jami’anta suka fara dukan mutane da ababen hawa bisa rashin girmama Madam, har sai da shi Abba ya shiga dakin jira ya same ta tare da korafi bisa abinda jami’an tsaro suka aikata ga mutanensa.

 

LABARAI MASU NASABA

MURIC Ba Ta Gamsu Da Rahoton Lafiyar El-Rufai Da Aka Gabatar A Kotu Ba

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Wata majiya ta bayyana cewa, yayin da Abba ke mata bayani, sai ta fara fadar maganganu marasa dadi akansa, dukda wani babban jami’i na bata hakuri, amma ta cigaba har tana mai cewa, ba zata bari Abba ya zama gwamnan jihar Kano ba, kamar yadda majiyar ta bayyana.

 

Lamarin ya ƙara zafi ne yayin da ta ga wani hadimin Abba mai suna Garba Kilo yana daukar bidiyo a wayarsa, nan ta ke ta umarci jami’ai su hallaka shi kuma ba abinda zai faru.

 

Madam Aisha ta turje akan cewa ba zata hau jirgi guda da Abba ba, wanda a karshe DPO na yan sanda dake filin jirgin ya hallara, tare da karɓar bayanai daga bangaren shi Abba akan lamarin da ya faru.

 

Amma bisa mamaki, yayin da DPO ya koma ga bangaren Madam Aisha domin karbar bayanai, sai bata bashi bayanin komai ba, tana mai cewa, “ka san ni wacece? Waye kai da zaka zo kana cewa na rubuta bayanai?” Haka DPO ya tafi ba tare da karɓar bayanai daga bangaren ta ba, kamar yadda majiyar ta bayyana.

 

Ana zargin Madam Aisha da amfani da jama’ai a wasu al’amura nata, domin ko kwanakin baya an zarge ta da bada umarnin dukan wani mai yi mata dinki (Tela) a Abuja, sakamakon rashin kammala mata aiki akan lokaci.

 

Har kawo yanzu dukkan bangarorin guda biyu basu ce komai akan lamarin ba.

Daga shafin: Nasara Radio 98.5 FM Kano

Abba Gida-gida
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela
  • Sulaiman
    Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
  • Sulaiman
    Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
  • Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

MASU ALAKA

Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i
Labarai

MURIC Ba Ta Gamsu Da Rahoton Lafiyar El-Rufai Da Aka Gabatar A Kotu Ba

July 7, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci
Manyan Labarai

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Next Post
Lokaci Ya Yi Da Za A Bai Wa Mata Dama, Ina Goyon Bayan Takarar Binani A Adamawa —Buhari

Lokaci Ya Yi Da Za A Bai Wa Mata Dama, Ina Goyon Bayan Takarar Binani A Adamawa —Buhari

LABARAI MASU NASABA

An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

July 7, 2026
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

MURIC Ba Ta Gamsu Da Rahoton Lafiyar El-Rufai Da Aka Gabatar A Kotu Ba

July 7, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.