ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Boko Haram Damfara Ce Da Aka Shirya Don Tarwatsa Nijeriya Kawai -Buhari

by Muhammad Maitela
4 years ago
Boko haram

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa, Boko Haram ba komai ba ce illa damfara da aka shirya domin tarwatsa Nijeriya.

Shugaban ya bayyana haka ne a yayin da ya karbi bakuncin Kungiyar Manyan Limaman Kiristoci na Katolika da ke Nijeriya (CBCN) a fadarsa da ke Abuja, inda ya kara da cewa, an samu ci gaba sosai kan sha’anin tsaron kasar nan.

  • Tinubu Ne Kadai Zai Iya Magance Rashin Tsaro Da Tabarbarewar Tattalin Arziki – Buhari 

“Ban jima na da dawowa daga Jihohin Adamawa da Yobe. Lokacin da nake ziyarar can, na ji abubuwan da mutane suke fada, haka nan jami’an gwamnati. Dukkansu sun ce an samu ci gab ana yanayin da ake ciki daga 2015, musamman a Jihar Borno.

ADVERTISEMENT

“Boko Haram ba komai ba ce illa damfara da munakisa da aka shirya don tarwatsa Nijeriya. Babu ta yadda za a yi ka hana mutane neman ilimi, al’umma tana bukatar ta samu ci gaba ta bangaren ilimi da kaifin basira,” in ji shi.

A halin da ake ciki kuma, Shugaba Buhari ya ce kungiyoyin ‘yan ta’adda ba za su sake yin wani katabus da sunan tasiri ba, saboda yadda gwamnatinsa ta yi musu raga-raga, inda kuma ya bukaci ‘Yan Nijeriya su ci gaba da bai wa jami’an tsaro cikakken goyon baya da hadin kai tare da bin doka da oda.
Ya bayyana hakan a lokacin da ya ziyarci Fadar Sarkin Damaturu a Jihar Yobe, Mai Martaba Hashimi El-Kanemi II, a ziyarar aikin bude wasu manyan ayyukan da gwamnatinsa tare da na Jihar Yobe suka aiwatar. Ya kara da bayyana cewa, gwamnati za ta ci gaba da kare ‘yancin kowane dan Nijeriya wajen samun ilimi, musamman ‘yan gudun hijira wadanda rikicin Boko Haram ta gayyara.

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

”Wanda zan iya cewa wata hudu masu zuwa, zan bar ofis, kuma zan ci gaba da abubuwan da suka kamata, sannan kuma ina da burin zan koma gefe in yi ritaya cikin aminci.
”Dole mu gina kyakkyawar fata a zukatanmu game da kasarmu, saboda abu ne mai muhimmanci mu tabbatar cewa bangaren tsaro da tattalin arziki suna kan gaba a kan komai.

”Haka kuma abubuwa da daman gaske sun faru a matsayinta na kasa, wanda nake kara kira gareku ku ci gaba da juriya tare da tsayin-daka, domin ba zamu bari wani ya sake hargutsa mu ba,” in ji shi.

Dangane da yadda aka samu ci gaba a sha’anin tsaron Arewa Maso Gabas, shugaban Nijeriya ya yaba wa Gwamna Mai Mala Buni da takwaransa na Jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, bisa aiki tukuru wajen sake farfado da makarantu, asibitoci hadi da muhimman wuraren da ‘yan ta’adda suka lalata a jihohin.

Shugaba Buhari ya ce, ”Saboda akwai yunkurin da suka yi wajen ruguza Nijeriya baki daya, amma Allah bai yarda ba. Kuma cikin ikon Allah ga Nijeriya nan ta sake komawa yadda take a baya.”

Har wala yau, Buhari ya yaba da namijin kokarin sojojin Nijeriya tare da hadin gwiwa ‘yansanda bisa sadaukarwar da suka nuna wajen kare mutuncin Nijeriya.

Bugu da kari, Buhari ya nanata cewa a matsayinsa na wanda ya yi gwagwarmayar hadin kan Nijeriya a lokacin yakin basasa, babu yadda za a yi ga wanda ya tsinci kansa a wancan yanayin a ce zai amince wani mutum ya sake raba kan ‘yan kasa ba.”
A nashi bangaren, Gwamnan Jihar Yobe, Buni ya shaida wa shugaban kasa cewa, sakamakon kamarin rikicin Boko Haram, ita ma Fadar Sarkin Damaturu ba ta tsira daga mamayar ‘yan ta’addan ba.

”Haka zalika kuma, yau gashi zaman lafiya ya samu a kowane bangaren Jihar Yobe, babu wani yanki a jihar da yake a hannun mayakan Boko Haram.

”Wanda kafin hakan, a baya da za ka ajiye dala biliyan daya a wannan Fadar ka ce wani ya zo ya dauka, babu mutumin da zai yi kasadar zuwa kusa da ita. Amma bayan kasancewarka shugaban kasa, abin ya zama tarihi wanda al’ummar Jihar Yobe ke more ‘yancin zaman lafiya da suka samu.”
A nashi jawabin, Sarkin Damaturu ya bayyana godiyarsa ga shugaban kasa bisa inganta harkar tsaro a Nijeriya.

Ya ce, ”Saboda ko shakka babu mu a nan Jihar Yobe ganau ne dangane da kokarin da gwamnatinka ta yi na kawo ci gaba a kasa.”
Bayan ziyarar Fadar Sarkin Damaturu, tawagar Shugaba Buhari ta zarce wajen bude ayyukan da gwamnatin Jihar Yobe ta aiwatar da kuma wasu ayyuka wadanda ma’aikatar ‘yansanda ta aiwatar a jihar.

Ayyukan da suka hada da bude shalkwatar rundunar ‘yansanda, asibitin ‘yansanda tare da hanyoyi da makarantar sakandire ta ‘yansanda, wadanda aka kammala aikinsu a karkashin Safeto Janar, Usman Alkali Baba.

Har ila yau kuma, shugaban kasa ya bude filin jirgin sama (Muhammadu Buhari International Cargo Airport), kasuwar zamani a Damaturu, asibitin kula da lafiyar mata da yara a asibitin koyarwa ta Jami’ar Jihar Yobe, kana da bude rukunin gidaje 2600 wadanda jihar ta gina tare da makarantar Mega a rukunin gidaje na New Bra-Bra, wanda Gwamna Buni ya gina.

Boko haram
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Next Post
Ko Ayyana Goyon Baya Ga Dan Siyasa Da Wasu Ke Yi Zai Yi Tasiri?

Ko Ayyana Goyon Baya Ga Dan Siyasa Da Wasu Ke Yi Zai Yi Tasiri?

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.