• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Ayyana Goyon Baya Ga Dan Siyasa Da Wasu Ke Yi Zai Yi Tasiri?

by Aminu Nasir
3 years ago
in Bakon Marubuci
0
Ko Ayyana Goyon Baya Ga Dan Siyasa Da Wasu Ke Yi Zai Yi Tasiri?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nuna goyan bayan wani dan siyasa zai iya wayar da kan mai zabe a matakin kasa da jihohi na ‘yan takara wanda yakan kai ga cusa wa masu zabe ra’ayin wanda za su zaba da ya dace. Masu zabe da dama sukan kasance cikin rashin sani a lokacin da suka zo zaben dan takara saboda yadda ake bayyana masu ‘yan siyasa da kuma yadda tsarin siyasar take.

Bayani a kan rashin sani shi ne, yadda ake rarraba kan masu zabe. Wani bangare a kan wannan shi ne, dan takara da gangar sai ya je ya nemi wani fitaccen mutum ko sananne ko kuma wasu kungiyoyi sanannu su nuna goyon bayansa ta yadda za su rika amfani da shi wajen yakin neman zabe da suke yi.

  • Ka Da A Mika Ragamar Mulkin Nijeriya A Hannun Mara Lafiya – Peter Obi

Siyasar Nijeriya dai ta rarrabu ta bangaren addini da kabila da yanki da kuma jam’iyyun siyasa, wanda hakan ya sanya yake yi wa masu zabe matukar wahala kafin su nuna inda suka karkata. A saboda haka ne ya sanya masu zabe suke duba wanda aka nuna goyon bayansa da suka yi kamancececiya a daya daga cikin abun da suke so kuma suke bi.

Wadanda suke nuna goyon bayansu suna da matukar muhimmanci a kasa ana kuma girmama su sosai. A ko da yaushe ana jiran su nuna goyon bayansu ga wani dan takara ko wani tsari da ake yi, saboda ana ganin mutuncinsu da daukansu masu gaskiya ana kuma sonsu matuka. Su talakawan kasa a ko da yaushe suna jirann su ji wanda aka nuna goyon bayansa, kuma suna kushe duk wata kungiya ko wasu daidaikun mutane wadanda ba su cancanta ba, ko kuma ba sa ra’ayinsu.

Daga kudu, daya daga cikin dalilin nuna goyon bayan Atiku Abubakar da Chief Arthur Eze ya yi a wurin bikin kalankowa na Ofala tare da gwamna Charles Soludo da sauran sarakunan gargajiya.

Labarai Masu Nasaba

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

Arthur Eze ya bayyana cewa dan takarar shugaban kasar Nijeriya da ya cancanta a cikin kabilar Igbo shi ne Soludo. A halin yanzu duk wanda son ya inganta tattalin arzikin Nijeriya dole ya bi tsarin da Soludo ya yi. Ra’ayin Arthur Eze tsari ne na dogon lokaci ga wanda yake son ya amfanar da Nijeriya.

A wajensa da mutanensa, nuna goyon bayan wani zai iya haifar da matsala ga damar da Soludo ke da shi, wanda zai faru nan gaba. Shugabannin Igbo da mutanensa suna nan za su ci gaba da goyon bayan PDP.

Nuna goyon bayan da Yarima Eze ya yi ya kawo rarrabuwan kai na yadda kungiyar Ohanaeze Ndigbo ta yi a karkashin tutar kudanci da shugabannin kungiyar yankin tsakiya idan aka koma watan Nuwamba. Kungiyar ta hada kungiyoyin Afenifere da PANDEF da shugabannin Middle Belt. Wani nuna goyon bayan wanda za a zaba wanda ya kara raba masu zabe shi ne, bangare na kungiyar Afenifere da suka ayyana cewa a zabi dansu, Bola Tinubu.

A daidai lokacin da ake rubuta wannan nazari, Tsohon Shugaban kasa , Obasanjo ya ayyana goyon bayansa ga Peter Obi ne. A cikin wani rubutun kundi da ya yi mai tsawon shafuka 6. Ya yi rubutu ne a kan matasan Nijeriya. Na sami wasikar da ya rubuta wanda ya fi karfin matasa masu zabe.

Hanyar sadarwar da aka yi amfani da shi ba a tsara shi ta yadda sakon zai kai gare su ba, kuma ma ‘yan kalilan ne daga cikinsu suke da hakurin da za su karanta rubutu da suka fi kalmomi 280.

A tunanin Obasanjo yana ganin kamar matasa ba a kyauta masu. Can sai na tuna da irin kiyayyar da ke tsakaninsa da ‘ya’yansa Gbenga da Iyabo. Iyabo ta taba rubuta wa mahaifinta wasika na rashin adalcinsa da san kai wanda ba ta jin dadinsa. Ko ma da mene ne wannan rudani na Obasanjo da kuma nuna goyan bayansa ga wani bai sami goyon kowani manyan tofaffin sojoji ba.

A ‘yan gaba-gaban Arewa kuwa, Yakubu Dogara da kungiyar Kiristocin Arewa an ji sun nuna goyon bayansu ga jam’iyyar PDP da ke yankinsu. Sai dai wanda ya fandare shi ne, Babachir Lawal wanda gwamnatin Buhari ta kora bisa almundahana na kwangilar cire ciyawa.

Ya yanke shawarar ya goyi bayan Peter Obi, bayan da Tinubu ya ki amsar bukatarsa na ba shi mukamin minista bayan an sami nasara. A wata hira da ya yi da sashin Hausa Muryar Amurka da gidan talabijin na Channels ya nuna rashin zamansa na nagartacce.

Kungiyar Izala ta JIBWIS wadanda ake dakon jiran jin wanda za su ayyana a goyi bayansa. Haka kuma Shugaban kungiyar, Abdullahi Bala Lau ya fara nuna inda ya karkata. Kamar shi ma Kabir Gombe. Dukkaninsu suna da kusan ra’ayi irin na Babachir, sai dai sun fi karkata ga Tinubu.

Mataimakin shugaban JIBWIS, Sheikh Yusuf Sambo Rigachikum ya nuna cewa Arewa ne ya kamata a sami shugaban kasa. Ba kamar Bala Lau da Kabir Gombe ba, Sheikh Yusuf Sambo Rigachikum yana ganin a rika bayyana wa mutane masu zabe sanin abubuwan da ya kamata su sani.

Nuna goyan bayan wani dan takara da ayyana shi yanzu aka fara. Zabe na karatowa za a rika jin ayyana goyon bayan ‘yan takara mabambanta. Kungiyar Kiristaoci na Nijeriya da manyan cocina har yanzu ba su ayyana goyon bayan dan takara daya tilo da za a zaba ba. Kungiyar Jame Ibori ba ta ayyana dan takararta ba, wanda masu zabe a yankin Kudu maso Kudu za su zaba.

Kungiyar Arewa ana jiran a ji dan takara daya tilo da za ta ce a goyawa baya, kamar yadda suka yi a lokacin da suka gayyaci ‘yan takarar shugaban kasa 6 a watan Oktoba 2022, a karkashin Gamayyar Kwamitin Arewa.

Ayyana dan takara da za su goyi baya babu shakka zai tabbatar da cewa zaben da za a yi za a yi a tsakanin yankuna uku na kasar nan ne. Kungiyoyin za su kasance tare da tsofaffin shugabannin kasa da wasu manyan sojoji masu murabus.

Wani abu na nuna goyon baya ga wani dan takara da masu zabe za su duba shi ne, wanda bijirarrun gwamnonin PDP 5 din nan da suka hada da Wike da Ortom da Ikpeazu da Ugwuanyi da Makinde. Duk da yake dai Wike ya ce zai sanar da matsayarsu na wanda za su zaba a watan Janairu. Jaridu sun ruwaito cewa sun yi taro da Tinubu a Landan, amma kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC ya karyata wannan rahoton.

Ta tabbata cewa wadannan gwamnoni 5 ba su da alkibla wanda karara ta nuna cewa ba su ma san abun da suke so ba ko kuma zai amfane su. Haka kuma zawarcin da suke yi wa ‘yan takarar shugaban kasa 4 ya nuna cewa ba su san abun da suke so ba. Duk da yake a nan dimokuradiyya ne kuma abun da suka yi bai saba da tsarin doka ba.

Masu zabe wadanda suke bibiyan abubuwan da suke yi sun gane cewa ba mutane ba ne masu alkibla. Haka kuma duk tsayayyen dan siyasa da ya san abun da yake yi zai kaucewa kawance da ire-irensu. Za a Iya fahimtar dalilin da ya sa Atiku ya yi watsi da su.

A saboda haka, wanda suke ayyana wanda za a zaba su sani cewa masu zabe suna son su ji abun da suke fada ne, amma ba za su yi aiki da abun ba.

Za su iya daukan cewa masu zabe ba su san abun da suke yi ba, amma kuma mafi yawan masu zabe sukan kauce wa wadanda suka san ba su dace ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Boko Haram Damfara Ce Da Aka Shirya Don Tarwatsa Nijeriya Kawai -Buhari

Next Post

Goron Juma’a

Related

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan
Bakon Marubuci

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

3 days ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

5 days ago
Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata
Bakon Marubuci

Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

1 week ago
Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari
Bakon Marubuci

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

1 month ago
Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus
Bakon Marubuci

Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

2 months ago
Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 
Bakon Marubuci

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

2 months ago
Next Post
Goro

Goron Juma’a

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.