• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Zamfara Ta Gano Likitocin Bogi 199 A Jihar

by Sadiq
3 years ago
Zamfara

Gwamna Bello Matawalle, ya ce gwamnatin Jihar Zamfara ta gano akalla likitocin bogi 199 da ke cikin tsarin biyan albashin ma’aikatan gwamnatin jihar.

Matawalle ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a garin Maradun, hedikwatar karamar hukumar Maradun ta jihar.

  • Mutum Daya Ya Mutu A Rikicin Fulani Da Patigi A Kwara 
  • Zargin Sace 89trn: Dan Takara A Kano Zai Maka Buhari A Kotu

A cewar gwamnan, duk da cewa gwamnatin jihar na biyan albashi ga likitoci 280 duk wata, amma ta gano likitoci 81 ne kawai ke aiki a fadin jihar.

Ya kuma bayyana cewa tuni ya gana da kungiyar kwadago ta NLC reshen jihar kan yadda za a gano wadancan likitocin bogi 199 da suka dauki tsawon lokaci suna karbar albashi ba bisa ka’ida ba.

Matawalle ya bayyana cewa, gano likitocin bogin ya biyo bayan ci gaba da binciken bayanan da ake yi wa daukacin ma’aikatan jihar ta ofishin shugaban ma’aikatan jihar.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

An ce aikin tattara bayanan na nuni ne da shirin gwamnatin jihar na fara aiwatar da tsarin mafi karancin albashi na Naira 30,000 ga ma’aikatan jihar.

“Matsalar ita ce, da zarar mun ce za mu aiwatar da shi (N30,000), ba za mu iya cewa za mu biya mutane kai tsaye haka ba. A’a, akwai tsari,” in ji Matawalle.

“Mun samar da tsari, kuma abin takaici, a lokacin aiki, an gano cewa akwai likitoci sama da 280 da suke karbar albashi daga gwamnatin jihar nan, amma a gaskiya muna da likitoci 81 ne kawai na gaskiya a Jihar Zamfara.

“Kungiyar kwadago ta tabbatar min dalilin da ya sa suka jinkirta shirin – cewa suna son tabbatar da cewa abubuwa sun tafi daidai saboda ba za mu iya ci gaba da hakan a matsayin gwamnati ba.”

Ya kuma tabbatar wa da jama’a cewa babu wani ma’aikaci na gaskiya da gwamnatinsa za ta yi murabus dangane da aiwatar da mafi karancin albashi na N30,000.

“Ba zan sake mayar da kowa ba. A gaskiya zan ba su gidajen (ma’aikatan gwamnati) na duk ma’aikatan gwamnati. Na gina musu gidaje 450 wadanda babu wanda ya san su, amma ranar Lahadi zan ba su makullin,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Next Post
Gobara Ta Kone Hedikwatar ‘Yansanda A Kano

Gobara Ta Kone Hedikwatar 'Yansanda A Kano

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 10, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho

October 10, 2025
Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

October 10, 2025
peter

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

October 10, 2025
Jonathan

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

October 10, 2025
Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

October 10, 2025
Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

October 10, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.