• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zabe: CBN Ya Musanta Shirin Katse Hada-Hadar Kudi Ta Intanet 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Zabe: CBN Ya Musanta Shirin Katse Hada-Hadar Kudi Ta Intanet 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da ake ci gaba da fuskantar tsaiko wajen tura kudi ta intanet da kuma amfani da na’urar cirar kudii ta PoS, Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya musanta bayanan da ake yadawa cewar ya bayar da umarnin katse hanyoyin tura kudi ta intanet a lokacin zaben da za a yi a ranar Asabar.

Labarin ya jefa fargaba a zukatan mutane har ta kai mutane sun fara rige-rigen zuwa kasuwanni domin tanadar abubuwan bukata kamar abinci da man fetur domin ajiye su a gida har zuwa lokacin da za a kammala zabe.

  • Zabe: ‘Yan Siyasa Sun Boye Tsofaffin Kudi Sama Da Biliyan 500 Ba Su Mayar CBN Ba – Bawa
  • INEC Ta Haramtawa Masu Zabe Amfani Da Wayar Salula Yayin Kada Kuri’a A Rumfar Zabe

Labarin da ya karade ko ina musamman a kafar WhatsApp.

A ranar Laraba ne dai CBN ya karyata rahotannin da ake ta yadawa ba tare da yin karin haske kan batun ba.

A sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter, CBN ya ce babu gaskiya a labarin katse Intanet kuma ba daga wurinsa sanarwar ta fito ba.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

Canjin kudi a Nijeriya dai ya janyo cece-kuce a bangarori da dama tun bayan fara aiwatar da tsarin a Disambar 2022.

Lamarin dai ya sa an yi ta samun bayanai na karya kan tsarin sakamakon rashin fitowar Babban Bankin Nijeriya na kin yi wa mutane bayani dalla-dalla game da manufarsa ta bijiro da shi.

Rarrabuwar kan da aka samu kan batun saka wa’adin mayar da tsofaffin takardun kudi zuwa ga batun ci gaba da amfani da su da kuma bayanan da aka rika samu daga bankuna sun jefa jama’a cikin fargaba da kuma rashin sanin alkiblar da za su bi.

Daga cikin irin wadannan bayanai masu janyo rudani da aka yi ta yadawa a baya-bayan nan akwai wanda ke cewa za a ci gaba da amfani da tsofaffin takardun kudi na N500 da N1000 har zuwa 1 ga watan Mayun 2023.

Sai dai kotun kolin da ke sauraren shari’ar da gwamnonin APC suka shigar ta sake dage zaman har zuwa ranar 1 ga watan Maris mai zuwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CBNHada-Hadar KudiIntanet
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zabe: ‘Yan Siyasa Sun Boye Tsofaffin Kudi Sama Da Biliyan 500 Ba Su Mayar CBN Ba – Bawa

Next Post

Wajibi Ne A Gudanar Da Bincike Na Gaskiya Game Da Lamarin Bututun “Nord Stream”

Related

Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

4 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

6 hours ago
Likitoci
Manyan Labarai

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

7 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

11 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

19 hours ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

23 hours ago
Next Post
Wajibi Ne A Gudanar Da Bincike Na Gaskiya Game Da Lamarin Bututun “Nord Stream”

Wajibi Ne A Gudanar Da Bincike Na Gaskiya Game Da Lamarin Bututun “Nord Stream”

LABARAI MASU NASABA

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

September 14, 2025
Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

September 14, 2025
An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

September 14, 2025
Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

September 14, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

September 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

September 14, 2025
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

September 14, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.