• English
  • Business News
Thursday, May 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Fara Gwagwarmayar Neman Shugabancin Majalisun Kasa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
majalisar kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani wani yanayi na ba-zata, za a kaddamar da majalisar kasa ta 10 a ranar Talata, 13 ga watan Yunin 2023, kwana biyu bayan wa’adin majalisar ta 9 zai kare a  ranar Lahadi 11 ga watan Yuni.

Idan za a iya tunawa cewa majalisar dokoki ta kasa mai ci an bude ta ne a ranar 11 ga watan Yunin 2019. Tsawon rayuwarta zai kare ne a ranar 11 ga watan Yunin 2023 wato Lahadi, ranar da ba a yin aiki, yayin ranar 12 ga watan Yuni ya kasance ranar hutun dimokuradiyya.

  • 2023: Majalisar Dattawa Ta Kasa, Ta Tafi Hutun Wata Daya

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, mambobin majalisa ta 10 da aka zaba wadanda suka hada da sanatoci da ‘yan jamalisan wakilai za su karbi shaidar takararsu a ranakun Talata da Laraba 7 da 8 ga watan Fabrairu, bayan da aka bayyana su a matsayin wadanda suka lashe zaben ‘yan majalisar dokokin Nijeriya da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu.

Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, a ranar Asabar da ta gabata yayin wata ganawa da kwamishinonin zabe gabanin zaben Gwamna da na ‘yan majalisar jiha da za a yi a ranar 11 ga Maris, ya bayyana cewa ta fuskar wakilcin jam’iyya, majalisar kasa ta 10 mai zuwa ita ce mafi yawan bambancin tun 1999.

Ya ce a zuwa yanzu dai a majalisar dattawa, jam’iyyar APC mai mulki ta samu kujeru 57, yayin da babbar jam’iyyar adawa ta PDP ta samu kujeru 29.

Labarai Masu Nasaba

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

Sauran sun hada da APGA wacce ta samu guda, Jam’iyyar LP ta samu 6, Jam’iyyar NNPP ta samu 2, SDP ta samu 2, sai kuma YPP wacce ta samu daya.

A majalisar wakilai kuwa, APC ta lashe kujeru 162, PDP ta samu 102, APGA ta samu 4, LP ta samu 34, NNPP na da 18, SDP tana da 2, YPP ta samu 1, sannan kuma ADC ta samu 2.

Idan aka yi la’akari da wannan tsari na sama jerin yawan jam’iyyun, zaben shugabannin majalisun biyu na 10 zai yi matukar zama mai abun sha’awa.

Gabanin kaddamar da majalisar dokokin kasar karo na 10 a ranar 13 ga watan Yunin 2023, wasu zababbun ‘yan majalisa sun fara fafutukar neman shugabancin majalisar dattawa da shugaban majalisar wakilai.
Baya ga shugabancin majalisar dattawa da shugaban majalisan wakilai, sauran mukaman da za a nada sun hada da na mataimakin shugaban majalisar dattawa da mataimakin shugaban majalisar wakilai.

Sakamakon binciken LEADERSHIP ya nuna cewa an fara zawarcin ofisoshin a tsakanin jam’iyya mai mulki tare da zababbun ‘yan majalisar dattawa da zababbun ‘yan majalisar wakilai na jam’iyyar APC da ke kokarin ganin ba a sake kuskuren 2015 a zaben shugabannin majalisar ba, inda aka zabi Sanata Bukola Saraki a matsayin shugaban majalisar dattawa, sannan aka zabi Yakubu Dogara a matsayin shugaban majalisar wakilai sabanin zabin jam’iyya mai mulki.

Duk da cewa jam’iyyar APC mai mulki, wadda tabbas za ta samu rinjaye a majalisun biyu na 10, har yanzu ba ta fito da wani tsari na shiyya-shiyya ko raba madafun iko na gwamnati mai zuwa karkashin jagorancin Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ba, tuni wasu daga cikin zababbun ‘yan majalisar tuni suka shiga tattaunawa ta bayan fage domin samun manyan mukaman a majalisar dokokin kasar da za ta fara aiki a ranar 13 ga watan Yuni.

Wadanda suka nuna sha’awarsu na zama shugaban majalisar dattawa ta 10 sun hada da zababben Sanata Orji Uzor Kalu (daga Abia ta Arewa), zababben Sanata Godswill Akpabio (daga Akwa Ibom ta arewa masu yamma), zababben Sanata Ali Ndume (daga Borno ta Kudu), da Sanata Jibrin Barau (daga Kano ta arewa).

Yayin da Kalu, Ndume da Barau suka kasance mambobi a majalisan dattawa ta 9 a halin yanzu, sai dai shi Akpabio ya kasance dan majalisar dattawa ta 8, wanda ke shirin komawa majalisar dattawa na 10.

Sai dai LEADERSHIP ta yi amanna cewa shugaban majalisar dattawa na yanzu, Ahmed Lawan, dan jam’iyyar APC daga yankin Yobe ta Arewa zai so ya ci gaba da rike mukaminsa idan akasarin sanatoci suka mara masa baya. Amma lokaci ne kawai zai nuna.

A halin da ake ciki a majalisar wakilai kuwa, shugaban majalisan na yanzu, Femi Gbajabiamila, wanda ke zama na hannun daman zababben Shugaban kasa, Bola Tinubu, na iya son gwada sa’arsa don ya ci gaba da rike mukaminsa a majalisa mai zuwa. Zai hau kan tasirin Tinubu don yin hakan idan lokaci ya yi.

Kafin hakan ta faru, Gbajabiamila zai samu manyan abokan hamayyar da zai yi takara da su wadanda suka hada da Hon. Ado Doguwa daga Jihar Kano da Hon. Aliyu Betara daga Jihar Borno da kuma sauran jiga-jigan ‘yan majalisa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shin CBN Ya Umurci Bankuna Su Ba Da Tsafaffin Kudi?

Next Post

GORON JUMA’A

Related

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

5 days ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

5 days ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

4 weeks ago
Majalisun kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

4 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

4 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

1 month ago
Next Post
Goro

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

May 28, 2025
Miƙa Mulki Daga Buhari Zuwa Tinubu: Abubuwan Da Suka Fi Jan Hankali

Tinubu Ya Yi Ƙoƙari, Gyaran Nijeriya Aikin Kowa Da Kowa Ne – Buhari

May 28, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya

Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya

May 28, 2025
Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

May 28, 2025
Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

May 28, 2025
Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama

Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama

May 28, 2025
Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana

Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana

May 28, 2025
Gwamnatin Adamawa Ta Fitar Da Naira Biliyan 2.4 Domin Biyan Jarrabawar WAEC Da NECO

Adamawa Ta Amince Da Mafi Ƙarancin Albashi Na ₦70,000 Ga Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi 

May 28, 2025
Masu Bincike Na Sin Sun Cimma Sabon Sakamako A Fannin Saurin Sadarwa Tsakanin Tauraron Dan Adam Da Doron Duniya

Masu Bincike Na Sin Sun Cimma Sabon Sakamako A Fannin Saurin Sadarwa Tsakanin Tauraron Dan Adam Da Doron Duniya

May 28, 2025
An Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC

An Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC

May 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.