• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Mika Wa Almajiran El-Zakzaky Motocinsu Da Aka Kama

by Idris Umar
2 years ago
in Labarai
0
‘Yansanda Sun Mika Wa Almajiran El-Zakzaky Motocinsu Da Aka Kama
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata kotu a Jihar Kaduna ta umarci ‘yan sanda da su mayar wa mabiya Sheikh Ibrahim Zakzaky, ababen hawansu da ake rike musu tun bayan takaddamar da ta barke tsakanin sojoji da almajiran malamin a Zariya shekara bakwai da ta wuce.

Da ya ke zanta wa da manema labarai a lokacin da ake mika motoci da babura, Barista M. Abu, lauyan da ke wakiltar ‘yan Shi’a, ya bayyana cewa da yawan motocin sun lalace.

  • EFCC Ta Damke ‘Yan Damfarar Intanet 17 A Benue
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Dalibai Mata 2 A Jami’ar Zamfara

Ya ce, “Mun zo ofishin ‘yan sanda na MTD ne bisa hukuncin kotu da muka samu a madadin wadanda suka shigar da kara.

“Adadin ababen hawan da muka shigar da kara a kai ya kamata ya zarce adadin wadanda muka gani yanzu a nan. Ababen hawan da ke kasa a nan guda 67 ne kawai. Kuma ya kamata a ce sun fi haka. Ko wadanda muka gani a nan duk an lalata su. Bai kamata mu same su a wannan yanayin ba.

“Wadanda mafi yawa aka kwashe a gefen hanya da kuma gidan Malaminsu, Malam El-Zakzaky. Inda sojoji suka tattare musu ababen hawansu tare da kama mutane wanda suka mika wa rundunar ‘yan sanda domin gudanar da bincike tare da gurfanar da su domin yanke musu hukunci.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

“Amma a bangaren ababen hawansu wadanda aka ajiye a MTD, kuma ba a taba gabatar da su a gaban kotu ba a lokacin shari’a ba. Bayan wancan hukuncin mun dauki matakin ganin an bayar da ababen hawan amma hakan ya ci tura saboda wasu dalilai nasu dole ta sa muka shigar da kara kan hakan.”

Lauyan ya ce tun cikin shekarar 2022 kotun a karkashin mai shari’a A. A Amina ta bayar da umurin bayar da ababen hawan, “daga lokacin da kotun ta bayar da umarni zuwa yanzu ya dauki lokaci”, in ji shi.

Lauyan ya tabbatar da cewa za su duba matakin da za su dauka a gaba duba da cewa ababen hawan da aka ba su ba su kai wadanda suka shigar da kara suna nema ba.

Malam Sidi Muhammad Rabiu mazaunin garin Kaduna, ya ce; “Kayayyakin kamar yadda muka zo muka same su da yawansu an cire abubuwan da suke cikin babura da motoci, an cire injinansu. Mafi yawan kayayyakin sai dai ka dauki gwangwanin mota ko babur.”

Idan za a tuna dai biyo bayan faruwar lamarin na Zariya da ya wakana a watan Disamban 2015 daruruwan almajiran Sheikh Ibrahim Zakzaky ne suka rasa ransu sakamakon arangama da sojoji.

Lamarin ta kai ga tsare Zakzaky da matarsa da wasu mabiya na tsawon shekaru daga bisani aka sake su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan SandaEl-ZakzakyHukunciKotuZariya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Mutum 17 Don Mika Mulki Ga Gwamnati Mai Jiran Gado

Next Post

An Kaddamar Da Taron Shekara Shekara Na Sadarwar Latirori Na Sin Karo Na 16

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

6 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

7 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

8 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

9 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

10 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

13 hours ago
Next Post
An Kaddamar Da Taron Shekara Shekara Na Sadarwar Latirori Na Sin Karo Na 16

An Kaddamar Da Taron Shekara Shekara Na Sadarwar Latirori Na Sin Karo Na 16

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.