ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Mika Wa Almajiran El-Zakzaky Motocinsu Da Aka Kama

by Idris Umar
3 years ago
Almajiran

Wata kotu a Jihar Kaduna ta umarci ‘yan sanda da su mayar wa mabiya Sheikh Ibrahim Zakzaky, ababen hawansu da ake rike musu tun bayan takaddamar da ta barke tsakanin sojoji da almajiran malamin a Zariya shekara bakwai da ta wuce.

Da ya ke zanta wa da manema labarai a lokacin da ake mika motoci da babura, Barista M. Abu, lauyan da ke wakiltar ‘yan Shi’a, ya bayyana cewa da yawan motocin sun lalace.

  • EFCC Ta Damke ‘Yan Damfarar Intanet 17 A Benue
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Dalibai Mata 2 A Jami’ar Zamfara

Ya ce, “Mun zo ofishin ‘yan sanda na MTD ne bisa hukuncin kotu da muka samu a madadin wadanda suka shigar da kara.

ADVERTISEMENT

“Adadin ababen hawan da muka shigar da kara a kai ya kamata ya zarce adadin wadanda muka gani yanzu a nan. Ababen hawan da ke kasa a nan guda 67 ne kawai. Kuma ya kamata a ce sun fi haka. Ko wadanda muka gani a nan duk an lalata su. Bai kamata mu same su a wannan yanayin ba.

“Wadanda mafi yawa aka kwashe a gefen hanya da kuma gidan Malaminsu, Malam El-Zakzaky. Inda sojoji suka tattare musu ababen hawansu tare da kama mutane wanda suka mika wa rundunar ‘yan sanda domin gudanar da bincike tare da gurfanar da su domin yanke musu hukunci.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

“Amma a bangaren ababen hawansu wadanda aka ajiye a MTD, kuma ba a taba gabatar da su a gaban kotu ba a lokacin shari’a ba. Bayan wancan hukuncin mun dauki matakin ganin an bayar da ababen hawan amma hakan ya ci tura saboda wasu dalilai nasu dole ta sa muka shigar da kara kan hakan.”

Lauyan ya ce tun cikin shekarar 2022 kotun a karkashin mai shari’a A. A Amina ta bayar da umurin bayar da ababen hawan, “daga lokacin da kotun ta bayar da umarni zuwa yanzu ya dauki lokaci”, in ji shi.

Lauyan ya tabbatar da cewa za su duba matakin da za su dauka a gaba duba da cewa ababen hawan da aka ba su ba su kai wadanda suka shigar da kara suna nema ba.

Malam Sidi Muhammad Rabiu mazaunin garin Kaduna, ya ce; “Kayayyakin kamar yadda muka zo muka same su da yawansu an cire abubuwan da suke cikin babura da motoci, an cire injinansu. Mafi yawan kayayyakin sai dai ka dauki gwangwanin mota ko babur.”

Idan za a tuna dai biyo bayan faruwar lamarin na Zariya da ya wakana a watan Disamban 2015 daruruwan almajiran Sheikh Ibrahim Zakzaky ne suka rasa ransu sakamakon arangama da sojoji.

Lamarin ta kai ga tsare Zakzaky da matarsa da wasu mabiya na tsawon shekaru daga bisani aka sake su.

Almajiran
Idris Umar
+ postsBio
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

MASU ALAKA

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya
Rahotonni

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati
Labarai

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare
Labarai

Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare

June 12, 2026
Next Post
An Kaddamar Da Taron Shekara Shekara Na Sadarwar Latirori Na Sin Karo Na 16

An Kaddamar Da Taron Shekara Shekara Na Sadarwar Latirori Na Sin Karo Na 16

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.