• English
  • Business News
Saturday, May 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Afrika Sun Ce Wa Kasar Amurka “Babu ruwanki”

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasashen Afrika Sun Ce Wa Kasar Amurka “Babu ruwanki”
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abokai na, kun fahimci damuwar iyayen yara kuwa? Wato yadda suke damuwa kan wasu abubuwan da yaransu ke yi, kamar son wasa maimakon yin karatu, da yawan mu’amala da wayar salula, da dai sauransu, abin da kan sa su zagin yara. Wannan damuwa ce da za a iya fahimta. Sai dai abin mamaki shi ne, wasu kasashe ma su kan nuna wannan nau’in damuwa na iyaye. Wato su kan kalli kansu tamkar “iyayen” sauran kasashe, inda suke son tsoma baki a harkokin cikin gida na sauran kasashen. 

Misali, lokacin da Kamala Harris, mataimakiyar shugaban kasar Amurka, take ziyara a kasar Ghana a kwanakin baya, ta matsawa bangaren Ghana lamba kan batun kare hakkin ‘yan luwadi. Dalilin da ya sa haka, shi ne domin majalisar dokokin kasar Ghana na tattaunawa kan daftarin dokar haramta masu neman jinsi daya. Dangane da wannan batu, Harris ta nuna goyon baya ga‘yan luwadi, inda ta ce, “ A ganin kasar Amurka, batun kare hakkin‘yan luwadi, wani batu ne da ya shafi hakkin dan Adam, don haka kasarmu ba za ta taba ja da baya ba.”

  • Afirka Ta Kudu Na Maraba Da Zuwan Sinawa Masu Yawon Shakatawa Kasar

Mun san kasar Amurka ta saba da yin katsalandan cikin harkokin gida na sauran kasashe, har ma da daukar matakan soja kan sauran kasashe, ta hanyar fakewa da kalmar “kare hakkin dan Adam”. Saboda haka kasar ba ta ganin wani kuskure a maganar Madam Harris. Sai dai kalaman nata ya fusata ‘yan kasar Ghana, inda Alban Bagbin, shugaban majalisar dokokin kasar Ghana, ya ce ba zaitaba yarda da maganar Madam Harris ba. A cewarsa, kasar Amurka na neman baiwa kasar Ghana umarni ne, lamarin da ya sabawa ruhi na Demokuradiyya.

Sa’an nan wani batu na daban da ya sa kasar Amurka damuwa shi ne huldar dake tsakanin kasashen Afrika da kasar ta Sin. Ko da yake, Kamala Harris ta ce ziyararta a nahiyar Afrika ba ta shafi kasar Sin ba. Amma rahotannin da kafofin watsa labaru na kasar Amurka suka gabatar sun nuna wata damuwa mai tsanani kan tasirin kasar Sin a kasashen Afirka. Inda kamfanin dillancin labaru na AP ya ce, lokacin da Madam Harris ke ziyara a kasar Zambia, jirgin samanta ya sauka a wani filin jirgin sama da wani kamfanin kasar Sin ya yi masa kwaskwarima, bisa rancen kudin da kasar Sin ta bayar. A nata bangare, jaridar The New York Times, ta ce ayarin motocin Harris ya wuce wata babbar mararrabar hanya dake tsakiyar birnin Accra na kasar Ghana, inda aka rubuta a wani kwali cewa, kasar Sin ce ta ba da tallafin kudin gina mararrabar hanyar. A cewar kamfanin AP, huldar kut-da-kut dake tsakanin Afrika da Sin ta sa gwamnatin kasar Amurka damuwa sosai, saboda tana tsoron ganin yadda kasashen Afirka suka kara karkata ga bangaren kasar Sin.

Wannan damuwa mai tsanani da kasar Amurka ta nuna ya ja hankali shugaba Nana Akufo-Addo na kasar Ghana, don haka ya mayar da martani. Yayin wani taron manema labaru, kuma a gaban Madam Kamala Harris, shugaban na kasar Ghana ya ce, “ Watakila kasar Amurka za ta damu game da tasirin kasar Sin a nahiyar Afrika, amma mu ba ma damuwa. Kasar Sin tana cikin dimbin kasashen da kasar Ghana ke hulda da su, ma iya cewa dukkan kasashen duniya abokanmu ne.” Ma’ana “Akwai dimbin kasashe a duniyarmu, kuma za mu iya hulda da duk wanda muke son hulda. Wannan batu ba ruwan kasar Amurka a ciki. ”

Labarai Masu Nasaba

Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa

Amurka Za Ta Girbi Abin Da Ta Shuka A Kan Matakin Soke Takardar Bizar Karatu Ga Dalibai Sinawa

Bayan haka, Yemi Osinbajo, mataimakin shugaban kasar Najeriya, shi ma ya wallafa wani bayani a shafinsa na sada zumunta na Twitter, inda ya ce, “Galibin kasashen Afrika ba za su nemi a yi musu afuwa bisa huldar kut-da-kut dake tsakaninsu da kasar Sin ba. Saboda kasar Sin ta gabatar da kanta a wurare da lokutan da su kasashen yamma ba su son kasancewa ciki. Kasashen Afrika na bukatar rancen kudi, da kayayyakin more rayuwa, sa’an nan kasar Sin ta biya musu bukatunsu.”

Gaskiya kasar Amurka ta sha nuna damuwa, inda ta damu da yiwuwar abkuwar“keta hakkin dan Adam” a kasashen Afrika, da yadda suke hulda da kasar Sin, da sauran batutuwa daban daban. Sai dai kasashen Afrika sun riga sun bayyana mata cewa, “Babu ruwanki ko kadan!”Wai mai Daki shi ya san inda yake masa Yoyo. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Bayar Da Belin Mawaki Portable

Next Post

Burundi Na Yabawa Tallafin Kasar Sin A Fannin Raya Noma

Related

Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa
Daga Birnin Sin

Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa

57 minutes ago
Amurka Za Ta Girbi Abin Da Ta Shuka A Kan Matakin Soke Takardar Bizar Karatu Ga Dalibai Sinawa
Daga Birnin Sin

Amurka Za Ta Girbi Abin Da Ta Shuka A Kan Matakin Soke Takardar Bizar Karatu Ga Dalibai Sinawa

11 hours ago
Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu
Daga Birnin Sin

Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu

19 hours ago
Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu
Daga Birnin Sin

Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu

20 hours ago
Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta
Daga Birnin Sin

Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta

21 hours ago
Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

23 hours ago
Next Post
Burundi Na Yabawa Tallafin Kasar Sin A Fannin Raya Noma

Burundi Na Yabawa Tallafin Kasar Sin A Fannin Raya Noma

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)

May 31, 2025
Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

May 31, 2025
Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa

Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa

May 31, 2025
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

May 31, 2025
Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

May 31, 2025
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

May 31, 2025
Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

May 31, 2025
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

May 31, 2025
Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115

Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115

May 31, 2025
Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica

Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica

May 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.