• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Majalisu Tara Da Ke Zawarcin Kujerar Gbajabiamila

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
‘Yan Majalisu Tara Da Ke Zawarcin Kujerar Gbajabiamila
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Adadin ‘yan majalisar wakilai da ke sa ido a kan kujerar shugaban majalisar wakilai ta 10 a yanzu ya kai tara.

Hakan dai na faruwa ne duk da cewa an sake zaben shugaban majalisar mai ci Femi Gbajabiamila a karo na shida kuma zai kasance a majalisar.

  • Ba A Taba Zabe A Nijeriya Mai Karancin Tashe-tashen Hankula Kamar Na 2023 Ba – Gwamnatin Tarayya

A watan Yunin shekarar 2019 ne dai aka kaddamar da majalisar wakilai mai ci a yanzu, kuma ana sa ran za a kaddamar da majalisa ta 10 a irin wannan wata na shekaran nan.

A ranar Talata ne, Abdulraheem Olawuyi dan majalisa mai wakiltar mazabar Ekiti/Isin/Irepodun/Oke-Ero a Jihar Kwara ya shirya bayyana sha’awar zama shugaban majalisar.

A cewar wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, ana sa ran Olawuyi zai bayyana aniyarsa ta neman kujerar ranar Talata a Abuja a hukumance.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

Olawuyi wanda shi ne shugaban kwamitin majalisar kan ba da agajin gaggawa da shirye-shiryen jinkai, ya ce ya yi tuntubar juna sosai kan aniyarsa ta tsayawa takarar shugabancin majalisa kuma ya ji dadin yadda ya samu goyon baya.

A cikin sanarwar mai taken, ‘AbdulRaheem ya shiga takarar shugaban majalisar, zai bayyana ranar 4 ga Afrilu a hukumance’, ya ce ya yi imanin cewa ya mallaki kwarewar da ake bukata don samun shugaban mai inganta idan abokan aikinsa suka zabe shi.
Ya ce tsofaffi da sabbin mambobin majalisar za su halarci sanarwar a hukumance.

“Ina mai tabbatar muku da cewa idan aka zabe ni, zan yi kokarin inganta manufofin da za su amfanar da daukacin ‘yan Nijeriya daga sassa daban-daban, kuma za mu yi aiki tare da dukkan bangarorin domin hada kan kasa. Ina matukar fatan haduwa da ’yan’uwana ’yan majalisa tare da bayyana musu ra’ayina, da kuma sauraron ra’ayoyinsu kan yadda za a inganta rayuwar jama’a idan aka zabe ni a matsayin shugaban majalisar wakilai,” in ji Olawuyi.

Dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Mallammadori/Kaugama a Jihar Jigawa kuma mataimakin shugaban kwamitin tsaro na majalisar, Abubakar Yalleman, ya bayyana aniyarsa ta zama shugaban majalisan wakilai a makon jiya.

Mataimakin shugaban majalisar, Ahmed Wase da shugaban masu rinjaye, Alhassan Ado-Doguwa da shugaban kwamitin majalisar kan harkokin sojojin ruwa, Yusuf Gagdi da shugaban kwamitin kasafin kudi na majalisar, Aliyu Betara da shugaban kwamitin majalisar kan cibiyoyin bincike na kimiyya, Olaide Akinremi da shugaban kwamitin majalisar kan harkokin yada labarai da hulda da jama’a, Benjamin Kalu da kuma shugaban kwamitin sufuri na kasa, Tajudeen Abbas, dukkansu suna cikin wadanda suka nuna sha’awarsu na neman shugabancin majalisar wakilai.

Wase ya fito ne daga Filato a shiyyar Arewa ta tsakiya, Ado-Doguwa ya fito daga Kano a Arewa maso Yamma, Gagdi yana wakiltar Filato a Arewa ta Tsakiya, Betara ya fito daga Borno a Arewa maso Gabas, Akinremi yana wakiltar Oyo a Kudu maso Yamma, Kalu daga Abiya a Kudu maso Gabas, Yalleman daga Jigawa a Arewa maso Yamma, sannan Abbas daga Kaduna a Arewa maso Yamma.
Sai dai kuma kan ‘yan majalisar ya rabu dangane da yankin da za a bai wa shugabancin majalisan a wannan karo.

Tuni dai Wase ya fara ziyartar manyan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC da ke fadin kasar nan, a wani bangare na kokarin nuna goyon baya ga burinsa.

Hakazalika, a bangaren majalisar dattawa kuwa, wasu mambobi biyu sun fito fili sun bayyana aniyarsu ta shugabancin majalisar. ‘Yan majalisan dai sun hada da shugaban masu rinjaye, Sanata Orji Kalu da kuma shugaban kwamitin kasafin kudi na majalisar dattawa, Jibrin Barau.

Tsohon shugaban marasa rinjaye, Sanata Godswill Akpabio da shugaban kwamitin ayyuka na majalisar dattawa, Sani Musa har yanzu ba su bayyana tsayawa takarar shugabancin majalisar ba a hukumance, amma masu goyon bayansu a ciki da wajen zauren majalisar sun yi ta magana a kansu.
Shugaban majalisar dattawa mai ci, Ahmad Lawan zai koma zauren majalisa a majalisa mai zuwa.

Shugabannin jam’iyya mai mulki na kasa sun gana da zababbun ‘yan majalisar tarayya a Abuja a ranar 6 ga Maris, 2023, inda aka tattaunawa a kan shugabancin karba-karba na shiyya-shiyya har zuwa bayan zaben gwamnoni da na majalisun jihohi da aka gudanar a ranar 18 ga Maris.

APC ba ta gana da zababbun ‘yan majalisar ba makonni biyu bayan kammala zaben.
A halin da ake ciki kuma, dan majalisar wakilai daga Jihar Kano, Shamsudeen Dambazau, ya bukaci jam’iyyar APC ta mika shugaban majalisar dattawa a yankin Arewa maso Yamma, yayin da ya kafe Jibrin ya hau kujerar.

Dambazau wanda ke wakiltar mazabar Takai/Sumaila ta Kano, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a mai taken ‘Majalisar Tarayya ta 10: Me ya sa APC ba za ta bayar da shugabancin majalisan dattawa ga yankin Arewa maso Yamma da kuma dalilin da zai sa Barau Jibrin zai iya zama shugaban majalisar dattawa na gaba, ya lissafo nasarorin da jam’iyyar ta samu a wannan yanki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Ya Gaza Gudanar Da Sahihin Zabe A 2023 – Kwankwaso

Next Post

An Samu Tsohuwar Hedimasta Da Laifin Yi Wa Dalibai Fyade

Related

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

12 hours ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 week ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
'Yan majalisu
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
Next Post
'Yan majalisu

An Samu Tsohuwar Hedimasta Da Laifin Yi Wa Dalibai Fyade

LABARAI MASU NASABA

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
'Yan majalisu

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.