• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Majalisu Tara Da Ke Zawarcin Kujerar Gbajabiamila

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
‘Yan Majalisu Tara Da Ke Zawarcin Kujerar Gbajabiamila
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Adadin ‘yan majalisar wakilai da ke sa ido a kan kujerar shugaban majalisar wakilai ta 10 a yanzu ya kai tara.

Hakan dai na faruwa ne duk da cewa an sake zaben shugaban majalisar mai ci Femi Gbajabiamila a karo na shida kuma zai kasance a majalisar.

  • Ba A Taba Zabe A Nijeriya Mai Karancin Tashe-tashen Hankula Kamar Na 2023 Ba – Gwamnatin Tarayya

A watan Yunin shekarar 2019 ne dai aka kaddamar da majalisar wakilai mai ci a yanzu, kuma ana sa ran za a kaddamar da majalisa ta 10 a irin wannan wata na shekaran nan.

A ranar Talata ne, Abdulraheem Olawuyi dan majalisa mai wakiltar mazabar Ekiti/Isin/Irepodun/Oke-Ero a Jihar Kwara ya shirya bayyana sha’awar zama shugaban majalisar.

A cewar wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, ana sa ran Olawuyi zai bayyana aniyarsa ta neman kujerar ranar Talata a Abuja a hukumance.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Olawuyi wanda shi ne shugaban kwamitin majalisar kan ba da agajin gaggawa da shirye-shiryen jinkai, ya ce ya yi tuntubar juna sosai kan aniyarsa ta tsayawa takarar shugabancin majalisa kuma ya ji dadin yadda ya samu goyon baya.

A cikin sanarwar mai taken, ‘AbdulRaheem ya shiga takarar shugaban majalisar, zai bayyana ranar 4 ga Afrilu a hukumance’, ya ce ya yi imanin cewa ya mallaki kwarewar da ake bukata don samun shugaban mai inganta idan abokan aikinsa suka zabe shi.
Ya ce tsofaffi da sabbin mambobin majalisar za su halarci sanarwar a hukumance.

“Ina mai tabbatar muku da cewa idan aka zabe ni, zan yi kokarin inganta manufofin da za su amfanar da daukacin ‘yan Nijeriya daga sassa daban-daban, kuma za mu yi aiki tare da dukkan bangarorin domin hada kan kasa. Ina matukar fatan haduwa da ’yan’uwana ’yan majalisa tare da bayyana musu ra’ayina, da kuma sauraron ra’ayoyinsu kan yadda za a inganta rayuwar jama’a idan aka zabe ni a matsayin shugaban majalisar wakilai,” in ji Olawuyi.

Dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Mallammadori/Kaugama a Jihar Jigawa kuma mataimakin shugaban kwamitin tsaro na majalisar, Abubakar Yalleman, ya bayyana aniyarsa ta zama shugaban majalisan wakilai a makon jiya.

Mataimakin shugaban majalisar, Ahmed Wase da shugaban masu rinjaye, Alhassan Ado-Doguwa da shugaban kwamitin majalisar kan harkokin sojojin ruwa, Yusuf Gagdi da shugaban kwamitin kasafin kudi na majalisar, Aliyu Betara da shugaban kwamitin majalisar kan cibiyoyin bincike na kimiyya, Olaide Akinremi da shugaban kwamitin majalisar kan harkokin yada labarai da hulda da jama’a, Benjamin Kalu da kuma shugaban kwamitin sufuri na kasa, Tajudeen Abbas, dukkansu suna cikin wadanda suka nuna sha’awarsu na neman shugabancin majalisar wakilai.

Wase ya fito ne daga Filato a shiyyar Arewa ta tsakiya, Ado-Doguwa ya fito daga Kano a Arewa maso Yamma, Gagdi yana wakiltar Filato a Arewa ta Tsakiya, Betara ya fito daga Borno a Arewa maso Gabas, Akinremi yana wakiltar Oyo a Kudu maso Yamma, Kalu daga Abiya a Kudu maso Gabas, Yalleman daga Jigawa a Arewa maso Yamma, sannan Abbas daga Kaduna a Arewa maso Yamma.
Sai dai kuma kan ‘yan majalisar ya rabu dangane da yankin da za a bai wa shugabancin majalisan a wannan karo.

Tuni dai Wase ya fara ziyartar manyan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC da ke fadin kasar nan, a wani bangare na kokarin nuna goyon baya ga burinsa.

Hakazalika, a bangaren majalisar dattawa kuwa, wasu mambobi biyu sun fito fili sun bayyana aniyarsu ta shugabancin majalisar. ‘Yan majalisan dai sun hada da shugaban masu rinjaye, Sanata Orji Kalu da kuma shugaban kwamitin kasafin kudi na majalisar dattawa, Jibrin Barau.

Tsohon shugaban marasa rinjaye, Sanata Godswill Akpabio da shugaban kwamitin ayyuka na majalisar dattawa, Sani Musa har yanzu ba su bayyana tsayawa takarar shugabancin majalisar ba a hukumance, amma masu goyon bayansu a ciki da wajen zauren majalisar sun yi ta magana a kansu.
Shugaban majalisar dattawa mai ci, Ahmad Lawan zai koma zauren majalisa a majalisa mai zuwa.

Shugabannin jam’iyya mai mulki na kasa sun gana da zababbun ‘yan majalisar tarayya a Abuja a ranar 6 ga Maris, 2023, inda aka tattaunawa a kan shugabancin karba-karba na shiyya-shiyya har zuwa bayan zaben gwamnoni da na majalisun jihohi da aka gudanar a ranar 18 ga Maris.

APC ba ta gana da zababbun ‘yan majalisar ba makonni biyu bayan kammala zaben.
A halin da ake ciki kuma, dan majalisar wakilai daga Jihar Kano, Shamsudeen Dambazau, ya bukaci jam’iyyar APC ta mika shugaban majalisar dattawa a yankin Arewa maso Yamma, yayin da ya kafe Jibrin ya hau kujerar.

Dambazau wanda ke wakiltar mazabar Takai/Sumaila ta Kano, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a mai taken ‘Majalisar Tarayya ta 10: Me ya sa APC ba za ta bayar da shugabancin majalisan dattawa ga yankin Arewa maso Yamma da kuma dalilin da zai sa Barau Jibrin zai iya zama shugaban majalisar dattawa na gaba, ya lissafo nasarorin da jam’iyyar ta samu a wannan yanki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Ya Gaza Gudanar Da Sahihin Zabe A 2023 – Kwankwaso

Next Post

An Samu Tsohuwar Hedimasta Da Laifin Yi Wa Dalibai Fyade

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

2 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

2 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

3 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

3 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

4 weeks ago
Next Post
'Yan majalisu

An Samu Tsohuwar Hedimasta Da Laifin Yi Wa Dalibai Fyade

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

August 10, 2025
Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

August 10, 2025
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

August 10, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

August 10, 2025
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

August 10, 2025
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

August 10, 2025
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.