• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jaridar Business Day Ta Karrama Gwamnan Gombe Kan Hidimta Wa Al’ummarsa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Jaridar Business Day Ta Karrama Gwamnan Gombe Kan Hidimta Wa Al’ummarsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jaridar ‘Business Day’ ta karrama Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, da lambar yabo na gwamna Mafi kwazo a fagen yi wa al’ummar jiharsa hidima. 

 

An gudanar da taron Bada lambar yabon gwarazan na shekarar 2022 ne a ranar Alhamis a Abuja Continental Hotel (Sheraton Hotel and Towers) yayin da mataimakin Gwamnan, Dr. Manassah Daniel Jatau ne ya karɓi kyaututtukan a madadinsa.

  • Tsare-Tsare Ga Ma’aikata: Gwamnonin Bauchi Da Gombe Sun Samu Babbar Lambar Yabo Daga Kungiyar Kwadago Ta TUC

Sauran fitattun mutanen da suka samu lambar yabo a bikin sun hada da Gwamnan Jihar Edo Godwin Obaseki, da Ministan Kwadago da Tallafi Chris Ngige, da Babban Daraktan Hukumar Bunmasa Fasahar Sadarwa ta Kasa NITDA, Kashifu Inuwa da dai sauransu.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

Mawallafi kuma shugaban kamfanin ‘Business Day Media’, Mr Frank Aigbogun, ya ce an shirya taron ne don karfafa gwiwar shugabanni a matakin jihohi su rungumi al’adar aiki tukuru, da samar da ribar demokradiyya ga al’umma.

 

A cewarsa, Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya fafata ne da wasu gwamnoni a bangarori daban-daban, kuma jihar sa ta zama zakara wacce tafi kowace jiha a fagen saukaka harkokin kasuwanci, kuma jihar da ta fi inganta yankunan karkara da birane.

 

“An cimma hakan ne bayan da kwamitin bada lambar yabon wanda ya kunshi fitattun mutane ya tattara bayanan da suka dace kai tsaye, da kuma nazarin sauran bayanan da aka tattara daga ɓangarori daban-daban na tattalin arziki da zamantakewa.

Business day

“Mun ga ci gaba sosai a Jihar Gombe tun bayan hawan Gwamna Inuwa Yahaya, mun ji irin nasarorin da ya samu a fannin kiwon lafiya, da samar da ababen more rayuwa, da raya karkara da zuba jari. A ‘yan kwanaki kadan da suka gabata mun ga yadda jihar sa ta samu matsayi na daya a fagen saukala harkokin da harkokin kasuwanci.

 

“Hakan bai zo mana da mamaki ba ganin yadda gwamnan yake ta lashe lambobin yabon da mukan bayar a kai a kai bayan shirya gasa, muna taya mai girma gwamna murna kuma muna kara masa kwarin guiwa kan ya ci gaba da irin wannan kokari nasa”.

 

Da yake karbar lambar yabon a madadin Gwamna Inuwa, Mataimakin nasa Dakta Manassah Daniel Jatau, ya bayyana karramawar a matsayin kalubalen da zai zaburar da shi wajen kara jajircewa kan aikin da ya saba.

 

Sai ya yaba wa kafar yada labaran bisa wannar karramawa ta aiki tukuru da nagarta a harkokin mulki.

 

“Zan fara da yaba wa Mawallafin wannar jarida ta Business Day bisa wannan karramawa da lambar yabo. Wannan wani aiki ne mai matukar muhimmanci da kuka yi. A makon daya gabatan nan muka samu lambar yabo a matsayin jiha mafi fice a fagen saukaka kasuwanci da kuma wani a matsayin gwamnati mafi haba-haba da ma’aikata, daga kungiyar Kwadago ta kasa TUC, kuma a yau ma ga shi muna sake samun wata lambar yabon na gwamnati mafi kwazo a fagen yiwa al’ummar ta hidima”.

 

“A gare mu, samun lambar yabo wani kalubale ne, nauyi ne da kuma tsammanin cewa za mu yi fiye da haka. Bisa tsari na fahimta, babu wanda zai iya yin komai shi kadai. Muna godiya da gudunmawar da kowa ke bayarwa a Jihar Gombe, musamman wadanda suka bada gudunmawa wajen samun wannar lambar yabo. Don haka mun sadaukar da wannar lambar yabo ga dokacin al’ummar jihar bisa irin gudunmawar da suka bayar wajen samun nasarar gwamnatin mu”.

 

“Ina gayyatar ku zuwa Jihar Gombe don ku ganewa idon ku cibiyar masana’antu ta Muhammadu Buhari mai girman kadada 1000, inda muka samar da duk abin da ake bukata da suka hada da wutar lantarki daga madatsar ruwa ta Dadinkowa, da ayyukan more rayuwa na zamani da abubuwan jin dadin jama’a da kuma zaman lafiya domin kasuwanci ya bunkasa. Ina kuma gayyatar ku da ku zo ku zuba jari a Jihar Gombe, muna da kyakkyawan yanayi na kasuwanci”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

FIFA Ta Yi Barazanar Kin Haska Kofin Duniya Na Mata A Wasu Kasashen

Next Post

Shugaban Kasar Sin Da Uwargidansa Sun Taya Sarki Charles Na III Da Sarauniya Camilla Murnar Nadin Da Aka Yi Musu A Hukumance

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

6 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

7 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

8 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

9 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

10 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

13 hours ago
Next Post
Shugaban Kasar Sin Da Uwargidansa Sun Taya Sarki Charles Na III Da Sarauniya Camilla Murnar Nadin Da Aka Yi Musu A Hukumance

Shugaban Kasar Sin Da Uwargidansa Sun Taya Sarki Charles Na III Da Sarauniya Camilla Murnar Nadin Da Aka Yi Musu A Hukumance

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.