• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rusau A Kano: APC Ta Bukaci Abba Ya Rushe Gine-ginen Da Kwankwaso Ya Sayar

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Rusau A Kano: APC Ta Bukaci Abba Ya Rushe Gine-ginen Da Kwankwaso Ya Sayar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar adawa ta APC ta bukaci gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano da ta kara wa’adin kwace wasu kadarori da rusa wasu a jihar zuwa wasu da  uban gidannsa Rabi’u Kwankwaso ya sayar.

Abba ya kasance mataimaki na musamman kuma daga baya ya zama kwamishinan Kwankwaso lokacin yana gwamnan jihar tsakanin 1999 zuwa 2003 da 2011 da 2015.

  • Gwamnan Zamfara Ya Ziyarci NADDC, Ya Nemi Hadin Gwiwar Bai Wa Matasan Jihar Horo
  • Jirgin Saman ‘Nigeria Air’ Damfara Ne —Shugaban Kamfanin Jiragen Sama

Kasa da sa’o’i 72 da rantsar da shi a ranar 29 ga watan Mayu, Abba ya ba da umarnin rusa wasu kadarorin da ya yi ikirarin cewa gwamnatin da ta gabata ta sayar da su ba bisa ka’ida ba.

Ya kuma yi ikirarin cewa an gina wasu kadarori a filayen gwamnati ba bisa ka’ida ba.

Tsakanin Asabar da Talata, gwamnati ta rushe gine-gine akalla guda hudu.

Labarai Masu Nasaba

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

A ranar Asabar din da ta gabata ma an rushe wani gini mai hawa uku mai shaguna 90 a yankin Nassarawa da ke jihar.

A wannan rana ne gwamnatin ta rushe Otal din Daula, otal din da gwamnatin Ganduje ta sayar tare da sake ginawa a karkashin tsarin hadin gwiwar wasu ‘yan kasuwa.

Gwamnatin ta kuma rushe wani gini a sansanin Alhazan jihar.

A ranar Litinin ne gwamnatin ta rushe shaguna a kasuwar Kantin Kwari; ta yi ikirarin cewa an gina shagunan ne a kan wani fili da aka sayar ba bisa ka’ida ba.

Sauran wuraren da aka ruwaito cewa an sawa jan fenti sun hada da Kasuwar Siyayya ta Shahuci, tsohon ginin Kamfanin jarida na Triumph, wanda aka sayar wa ‘yan kasuwa.

“Kaddarorin gwamnati a lamba 5, 6, da 7 a kan titin Bala Muhammed. Kadarorin gwamnati mai lamba 132 da ke titin Dawaki da lamba 13 a titin Ali Akilu gwamnatin Kwankwaso ce ta siyar da su.

“Kaddarorin gwamnati da ke lamba 193 da 194 da 196 da 197 da 198 da 920 duk a titin Ahmadu Bello gwamnatin Kwankwaso ce ta siyar da su, haka kuma Gwamna Ganduje ya yi amfani da su,” in ji Iliyasu.

APC ta yi ikirarin cewa Abba ne sakataren Kwankwaso, lokacin da aka sayar wadannan kadarorin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbbaAPCGandujekanoKwankwasoNNPPRusau
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Zamfara Ya Ziyarci NADDC, Ya Nemi Hadin Gwiwar Bai Wa Matasan Jihar Horo

Next Post

Kotu Ta Tura Magidanci Gidan Yari Kan Yi Wa Makocinsa Barazana A Kano

Related

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

4 hours ago
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

15 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

17 hours ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

22 hours ago
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

22 hours ago
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

1 day ago
Next Post
PDP A Kano: Kotu Ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Shari’ar Sadiq Wali Da Abacha

Kotu Ta Tura Magidanci Gidan Yari Kan Yi Wa Makocinsa Barazana A Kano

LABARAI MASU NASABA

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.