• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rusau A Kano: APC Ta Bukaci Abba Ya Rushe Gine-ginen Da Kwankwaso Ya Sayar

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Rusau A Kano: APC Ta Bukaci Abba Ya Rushe Gine-ginen Da Kwankwaso Ya Sayar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar adawa ta APC ta bukaci gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano da ta kara wa’adin kwace wasu kadarori da rusa wasu a jihar zuwa wasu da  uban gidannsa Rabi’u Kwankwaso ya sayar.

Abba ya kasance mataimaki na musamman kuma daga baya ya zama kwamishinan Kwankwaso lokacin yana gwamnan jihar tsakanin 1999 zuwa 2003 da 2011 da 2015.

  • Gwamnan Zamfara Ya Ziyarci NADDC, Ya Nemi Hadin Gwiwar Bai Wa Matasan Jihar Horo
  • Jirgin Saman ‘Nigeria Air’ Damfara Ne —Shugaban Kamfanin Jiragen Sama

Kasa da sa’o’i 72 da rantsar da shi a ranar 29 ga watan Mayu, Abba ya ba da umarnin rusa wasu kadarorin da ya yi ikirarin cewa gwamnatin da ta gabata ta sayar da su ba bisa ka’ida ba.

Ya kuma yi ikirarin cewa an gina wasu kadarori a filayen gwamnati ba bisa ka’ida ba.

Tsakanin Asabar da Talata, gwamnati ta rushe gine-gine akalla guda hudu.

Labarai Masu Nasaba

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari

A ranar Asabar din da ta gabata ma an rushe wani gini mai hawa uku mai shaguna 90 a yankin Nassarawa da ke jihar.

A wannan rana ne gwamnatin ta rushe Otal din Daula, otal din da gwamnatin Ganduje ta sayar tare da sake ginawa a karkashin tsarin hadin gwiwar wasu ‘yan kasuwa.

Gwamnatin ta kuma rushe wani gini a sansanin Alhazan jihar.

A ranar Litinin ne gwamnatin ta rushe shaguna a kasuwar Kantin Kwari; ta yi ikirarin cewa an gina shagunan ne a kan wani fili da aka sayar ba bisa ka’ida ba.

Sauran wuraren da aka ruwaito cewa an sawa jan fenti sun hada da Kasuwar Siyayya ta Shahuci, tsohon ginin Kamfanin jarida na Triumph, wanda aka sayar wa ‘yan kasuwa.

“Kaddarorin gwamnati a lamba 5, 6, da 7 a kan titin Bala Muhammed. Kadarorin gwamnati mai lamba 132 da ke titin Dawaki da lamba 13 a titin Ali Akilu gwamnatin Kwankwaso ce ta siyar da su.

“Kaddarorin gwamnati da ke lamba 193 da 194 da 196 da 197 da 198 da 920 duk a titin Ahmadu Bello gwamnatin Kwankwaso ce ta siyar da su, haka kuma Gwamna Ganduje ya yi amfani da su,” in ji Iliyasu.

APC ta yi ikirarin cewa Abba ne sakataren Kwankwaso, lokacin da aka sayar wadannan kadarorin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbbaAPCGandujekanoKwankwasoNNPPRusau
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Zamfara Ya Ziyarci NADDC, Ya Nemi Hadin Gwiwar Bai Wa Matasan Jihar Horo

Next Post

Kotu Ta Tura Magidanci Gidan Yari Kan Yi Wa Makocinsa Barazana A Kano

Related

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura
Manyan Labarai

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

10 hours ago
Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari

11 hours ago
Tinubu Ya Isa Katsina Don Tarbar Gawar Buhari
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Katsina Don Tarbar Gawar Buhari

11 hours ago
Buhari Na Cikin Ƙoshin Lafiya Kwana Ɗaya Kafin Rasuwarsa – Mamman Daura
Manyan Labarai

Buhari Na Cikin Ƙoshin Lafiya Kwana Ɗaya Kafin Rasuwarsa – Mamman Daura

11 hours ago
Buhari Da Ya Daɗe Da Rasuwa Idan A Asibitocin Nijeriya Ake Duba Shi – Adesina
Manyan Labarai

Buhari Da Ya Daɗe Da Rasuwa Idan A Asibitocin Nijeriya Ake Duba Shi – Adesina

12 hours ago
HOTUNA: An Tsaurara Tsaro A Gidan Buhari Da Ke Daura
Hotuna

HOTUNA: An Tsaurara Tsaro A Gidan Buhari Da Ke Daura

14 hours ago
Next Post
PDP A Kano: Kotu Ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Shari’ar Sadiq Wali Da Abacha

Kotu Ta Tura Magidanci Gidan Yari Kan Yi Wa Makocinsa Barazana A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

July 15, 2025
Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 15, 2025
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

July 15, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

July 15, 2025
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

July 15, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

July 15, 2025
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.