ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rusau A Kano: APC Ta Bukaci Abba Ya Rushe Gine-ginen Da Kwankwaso Ya Sayar

by Sadiq
3 years ago
APC

Jam’iyyar adawa ta APC ta bukaci gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano da ta kara wa’adin kwace wasu kadarori da rusa wasu a jihar zuwa wasu da  uban gidannsa Rabi’u Kwankwaso ya sayar.

Abba ya kasance mataimaki na musamman kuma daga baya ya zama kwamishinan Kwankwaso lokacin yana gwamnan jihar tsakanin 1999 zuwa 2003 da 2011 da 2015.

  • Gwamnan Zamfara Ya Ziyarci NADDC, Ya Nemi Hadin Gwiwar Bai Wa Matasan Jihar Horo
  • Jirgin Saman ‘Nigeria Air’ Damfara Ne —Shugaban Kamfanin Jiragen Sama

Kasa da sa’o’i 72 da rantsar da shi a ranar 29 ga watan Mayu, Abba ya ba da umarnin rusa wasu kadarorin da ya yi ikirarin cewa gwamnatin da ta gabata ta sayar da su ba bisa ka’ida ba.

ADVERTISEMENT

Ya kuma yi ikirarin cewa an gina wasu kadarori a filayen gwamnati ba bisa ka’ida ba.

Tsakanin Asabar da Talata, gwamnati ta rushe gine-gine akalla guda hudu.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

A ranar Asabar din da ta gabata ma an rushe wani gini mai hawa uku mai shaguna 90 a yankin Nassarawa da ke jihar.

A wannan rana ne gwamnatin ta rushe Otal din Daula, otal din da gwamnatin Ganduje ta sayar tare da sake ginawa a karkashin tsarin hadin gwiwar wasu ‘yan kasuwa.

Gwamnatin ta kuma rushe wani gini a sansanin Alhazan jihar.

A ranar Litinin ne gwamnatin ta rushe shaguna a kasuwar Kantin Kwari; ta yi ikirarin cewa an gina shagunan ne a kan wani fili da aka sayar ba bisa ka’ida ba.

Sauran wuraren da aka ruwaito cewa an sawa jan fenti sun hada da Kasuwar Siyayya ta Shahuci, tsohon ginin Kamfanin jarida na Triumph, wanda aka sayar wa ‘yan kasuwa.

“Kaddarorin gwamnati a lamba 5, 6, da 7 a kan titin Bala Muhammed. Kadarorin gwamnati mai lamba 132 da ke titin Dawaki da lamba 13 a titin Ali Akilu gwamnatin Kwankwaso ce ta siyar da su.

“Kaddarorin gwamnati da ke lamba 193 da 194 da 196 da 197 da 198 da 920 duk a titin Ahmadu Bello gwamnatin Kwankwaso ce ta siyar da su, haka kuma Gwamna Ganduje ya yi amfani da su,” in ji Iliyasu.

APC ta yi ikirarin cewa Abba ne sakataren Kwankwaso, lokacin da aka sayar wadannan kadarorin.

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Next Post
PDP A Kano: Kotu Ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Shari’ar Sadiq Wali Da Abacha

Kotu Ta Tura Magidanci Gidan Yari Kan Yi Wa Makocinsa Barazana A Kano

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.