• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Kebbi Ya Bukaci Maniyyatan Jihar Da Su Kasance Jakadu Nagari

by Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnan Kebbi Ya Bukaci Maniyyatan Jihar Da Su Kasance Jakadu Nagari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Nasir Idris, ya bukaci maniyyata aikin hajjin bana daga jihar Kebbi da su kasance jakadu nagari a tsawon zaman da suka yi a kasar Saudiyya yayin da suke gabatar da aikin hajjin bana.

 

Dakta Nasir Idris, ya bayar da wannan shawarar ne a lokacin da ya kai ziyarar bankwana da rukunin farko na maniyyata a sansanin alhazai da ke Birnin Kebbi, ya bayyana cewa, an san alhazan jihar da zama masu bin doka da oda, inda ya yi kira gare su da su kiyaye irin wannan dabi’a.

  • Hajjin Bana: Ku Zama Jakadu Na Kwarai – Gwamnan Gombe Ga Maniyyata

Ya sanar da su cewa wannan shi ne karon farko da gwamnati mai ci ta shirya tsarin gudanar da aikin Hajji kuma ta yi iya bakin kokarinta wajen ganin an gudanar da aikin jigilar mahajjata a filin jirgin sama na Sir Ahamadu da ke Birnin Kebbi amma hukumar ta aiyana cewa jirgin zai tashi ne a filin jirgin sama na Sakkwato.

 

Labarai Masu Nasaba

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Ya shawarci alhazai da su dauki irin wannan ci gaban a matsayin wani aiki na Allah inda ya ce shi ma zai yi aikin Hajjin bana tare da su don ba shi damar duba wuraren da ake bukatar gyara.

 

Gwamnan ya ba da tabbacin cewa an kammala duk wani shiri na jin dadi da jin dadin alhazai a kasar Saudiyya, sai dai ana jiran isowarsu kasa mai tsarki. Haka kuma ya bukaci mahajjatan da su kara himma wajen yi wa shugabannin kasa addu’ar samun nasara tare da samun zaman lafiya da ci gaba a Nijeriya.

 

A nasa jawabin, Amirul Hajj na jihar Kebbi na bana, tsohon ministan harkokin cikin gida, Janar Muhammadu Magoro, ya shaida wa gwamnan cewa an samar da komai domin ganin an gudanar da aikin Hajji cikin sauki.

 

Janar Magoro ya sanar da cewa likitoci goma sha takwas da adadin ma’aikatan lafiya da suka dace za su raka maniyyatan zuwa Saudiyya domin kulawa da bukatunsu na lafiya. Ya kuma kara da cewa an kafa kwamitoci goma sha hudu don tabbatar da jin dadin alhazai.

 

Matan Gwamnan jihar Kebbi Nasir Idris, Hajiya Zainab Nasir da Hajiya Nafisa Nasir sun bukaci maniyyata da su yi addu’a ga jihar da kasar Nijeriya yayin da suke a kasa mai tsarki.

 

A nata jawabin, Hajiya Zainab ta ce jerin laccoci da shirye-shiryen fadakarwa da karawa juna sani da aka yi wa mahajjata an yi su ne domin su tsara dabi’u da tunaninsu ta yadda za su fahimci mahimmanci da abubuwan da ke tattare da aikin hajji.

 

Ta bayyana cewa gwamnati ta yi tanadin isassun wuraren kwana, tsarin ciyarwa, kayan aiki, tallafin magunguna da sauran kayan agaji da za su samu nasarar gudanar da aikin hajji.

 

A nata bangaren, Hajiya Nafisa, ta bukaci alhazai da su kula da kayansu, ta kuma shawarce su da su yi taka-tsan-tsan wajen yin musanyar kudade a lokacin zamansu a kasar Saudiyya.

 

“Ya kamata ku tabbatar kun bar darussan da aka koya daga shirye-shiryen fadakarwa da laccoci daban-daban su shafi halayenku da kyau yayin gabatar da addu’o’i ga jihar Kebbi da kasar Nijeriya baki daya,” in ji ta.

 

Da yake jawabi a madadin mahajjatan, Ahmad Galadima daga karamar hukumar Argungu ya godewa gwamnan bisa tsarin da ya dace na gudanar da aikin Hajji


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Cire Tallafin Mai: Ina Jajanta Mu Ku, Sadaukarwarku Ba Za Ta Tafi A Banza Ba – Tinubu Ga ‘Yan Nijeriya

Next Post

An bankado Asirin Wasu Ma’aikatan Hukumar RMAFC Bisa Zargi Yin Kutse A Tsarin IPPIS

Related

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

14 minutes ago
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

2 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

2 hours ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

3 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

6 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

8 hours ago
Next Post
An bankado Asirin Wasu Ma’aikatan Hukumar RMAFC Bisa Zargi Yin Kutse A Tsarin IPPIS

An bankado Asirin Wasu Ma'aikatan Hukumar RMAFC Bisa Zargi Yin Kutse A Tsarin IPPIS

LABARAI MASU NASABA

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.