• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Halin ‘Yan Siyasa Na Ba Sarakuna Mamaki – Sarkin Zazzau

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Rahotonni
0
Halin ‘Yan Siyasa Na Ba Sarakuna Mamaki – Sarkin Zazzau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli ya bayyana cewa halin ‘yan siyasa na bai wa sarakuna mamaki.

Mamakin da suke yi wa ‘yan siyasa, a cewarsa shi ne, lokacin da ‘yan siyasa ke yakin nema zabe sai su zo wurinsu, amma da zarar sun samu nasara ba a kara jin duriyarsu sai bayan shekaru hudu. Ya kara da cewa sarakuna na bukatar samun matsayi a tsarin mulki ba wai saboda yukurin kirkiro wani bangare na gwamnati ba ne a cikin kasar nan.

  • Gwamnatin Kaduna Ta Tabbatar Da Bullar Cutar Diphtheria A Kafanchan

Sarkin Zazzau ya bayyana hakan ne a lokacin da shugaban majalisar wakilai, Rt. Hon Tajudeen Abbas ya ziyarce shi a fadarsa da ke Zariya ta Jihar Kaduna.

“Ba za a iya bata kwatanta irin gudummuwar da sarakuna suke bayarwa ba, saboda sarakuna suna taka muhimmiyar rawa tun fara mulkin dimokuradiyya har zuwa yau. Na san cewa mafi yawancinku a nan kuna da alaka da sakakuna ko ta kusa ko ta nesa.

“Abin da yake ba mu mamaki shi ne, mutane suna zuwa wurinmu neman tabarraki lokacin zabe, amma da zarar sun samu nasara, ba za su sake dawowa ba sai lokacin zabe kana su kara tuntubarmu. Kafin yanzu, muna mamakin yadda ake yi wa sarakuna haka, amma kuma sun kasa ganewa cewa su sarakuna a ko da yaushe suna nan kan mukaminsu, ko muna raye ko mun mutu. Duk inda mutum ya je sai ya dawo wurinmu.

Labarai Masu Nasaba

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

“Muna jin yadda wasu ‘yan siyasa ke cewa muna son kirkiro wani bangare na gwamnati. Ina magana amadadin sauran sarakuna kamar irinsu Mai Alfarma Sarkin Musulmi da Shehun Borno da sauran sarakuna. Mun tattauna kan wannan matsala babu adadi.

Mun je Abuja, inda muka gana da tsohon shugaban kasa da shugaban majalisar dattawa da shugaban majalisar wakilai. Mun gabatar da matsayinmu karkashin jagorancin Sarkin Lafiya wanda shi tsohon alkalin kotun koli ne. Mun zayyana matsayinmu, inda muka mika wa tsohon shugaban majalisar dattawa, mun yi mamakin yadda aka yi watsi da kudurin namu.

“Ina magana ne amadadin daukacin sarakunan Arewa. Muna fatan majalisar kasa da duba wannan kurin tare da aiki a kansa da kuma tabbatar ya zama doka.”
Ya kara da cewa babu abin da Masarautar Zazzau za ta iya cewa sai dai godiya ga Allah da ya azurtata.

Ya ce masarautar da kyankyashe shahararrun ‘yan Nijeriya tun daga kan tsohon shugaban kasa, Yakubu Gowon da tsohon mataimakin shugaban kasa, Namadi Sambo da ministoci da dama da sakatarorin gwamnatin tarayya, yanzu kuma ga shugaban majalisar wakilai.

Da yake jawabi, Rt. Hon Tajudeen Abbas ya sha alwashin cewa majalisa ta 10 za ta karkiri matsayin sarakuna a cikin kundin tsarin mulkin kasar nan.

Shugaban majalisar wakilai wanda shi dan asalin garin Zariya ne da yake wakiltar mazabar Zariya a zauren majalisa kuma yana da sarauta a cikin masarautar. Ya ce shi da kansa da kuma sauran ‘yan majalisan wakilai sun fahimci muhimmancin sarakuma, sannan za su tabbatar da cewa sun saka su a cikin kundin tsarin mulki.

“Tun shekaru uku da suka gabata na san cewa akwai takardar da majalisar sarakunan kasar nan suka gabatar, inda suka bayyana yadda sarakuna ya kamata su yi aiki a wannan zamani. Muna yi wa Allah godiya da ya kaddara danku ya zama shugaban majalisar wakilai kuma zai sake yin nazari kan matsayin sarakuna.

“Ina mai tabbatar muka cewa ni da suran ‘yan majalisa za mu sake bankado takardar da majalisar sarakuna ta rubuta domin tabbatar da cewa an sama aikin sarakuna a cikin kundin tsarinmulki.

“Za mu yi aiki kafada da kafada da dukkan majalisun kasa domin sake dawo da martabar sarakunan gargajiya.”
Ya nuna jin dadinsa ga sarkin da kuma daukacin mutanen masarautar Zazzau bisa wannan ziyara ta farko tun bayan da ya zama shugaban majalisar wakilai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bude Dandalin CMG Karo Na 2 A Shanghai

Next Post

‘Yansanda Sun Cafke Daliban Jami’a 3 Kan Kashe Direban Mota

Related

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

1 day ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

7 days ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

7 days ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

2 months ago
Next Post
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

'Yansanda Sun Cafke Daliban Jami'a 3 Kan Kashe Direban Mota

LABARAI MASU NASABA

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.