• English
  • Business News
Thursday, August 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Tinubu Da Atiku Ba Za Su Iya Gyara Nijeriya Ba — Ango Abdullahi

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
2023: Tinubu Da Atiku Ba Za Su Iya Gyara Nijeriya Ba  — Ango Abdullahi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jigo a cikin kungiyar dattawan arewa (NEF), Farfesa Ango Abdullahi ya bayyana cewa a halin yanzu da ake ciki, manyan ‘yan takarar shugaban kasa ba za su taba iya gyara Nijeriya ba.

Ya ce a cikin ‘yan takarar shugaban kasa da ke da su a halin yanzu, gwara ‘yan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar LP, Mista Peter Obi da na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Masu Kwankwaso kila za su iya tabuka wani abu, amma ‘yan takatar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu da na PDP, Atiku Abubakar ba za su iya tabuka komi ba.

  • NNPP Ta Kaddamar Da Kwamitin Sulhu Da Zaman Lafiya A Neja

Ya dai jaddada cewa wadannan ‘yan takara sun shafe shakara da shekaru suna gudanar da siyasa a Nijeriya ba tare da kawo wani sauyi ba. Ya ce da jam’iyyar APC ta bai wa Mataimakin Shugaban Kasa, Yemi Osinbajo takara zai iya cewa gwara-gwara, haka ma da PDP ta bai wa tsohon ma’aikacin banki, Mohammed Hayatu-Deen takara da zai iya ganin za a samun kwarrun ‘yan takarar shugabanin kasa.

Ango Abdullahi ya kara da cewa ba zai taba goyon bayan daya daga cikin wadannan ‘yan takararan shugaban kasa ba. Ya ce yana kira ga ‘yan Nijeriya su tashi tsaye wajen kalubalantar wadannan ‘yan takarar shugaban kasa domin ganin daya daga cikinsu bai hau karagar mulki ba a 2023.

Jigon ya bayyana hakan ne lokacin da yake zantawa da ‘yan jarida ta wayar salula a cikin makon da ya gabata.
Ya ce, “Har hanzu bai ga wani dan takara da zai iya gyara Nijeriya ba. ‘Yan takarar da muka da su a yanzu ba za su iya tabuka komi ba. Domin ta yaya za a iya cewa Tinubu da Atiku za su iya gyara Nijeriya.?
“Sun kashe shekaru 25 zuwa 30 suna gudanar da harkokin siyasa, amma babu wani abu da suka taba yi na gyara Nijeriya. To me za mu yi da wadannan ‘yan takara?
“Akwai mutanen da suka cancanta amma ba su aka bai wa takara ba saboda tsarin siyasan a gurbace take,” in ji shi.
Ya ci gaba da cewa yana kira ga ‘yan Nijeriya da su sani akwai matsaloli a Nijeriya kuma dole su da kansu ne za su iya samar wa kansu mafita a kan wadannan matsaloli wajen zaben shugaban kasan da ya dace a 2023.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Kuri’un ‘Yan Nijeriya Ne Za Su Yanke Hukuncin Lashe Zabe – INEC

Next Post

Yadda Buhari Ya Dakile Barazanar Da APC Ke Fuskanta A Majalisar Dattawa

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

3 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

3 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

3 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

4 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

4 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

1 month ago
Next Post
Buhari Ya Ce Ba Zai Nemi Wa’adi Na Uku Ba

Yadda Buhari Ya Dakile Barazanar Da APC Ke Fuskanta A Majalisar Dattawa

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16

Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16

August 14, 2025
Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina

Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina

August 14, 2025
Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

August 13, 2025
Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

August 13, 2025
APC

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

August 13, 2025
Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

August 13, 2025
Tinubu

Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 

August 13, 2025
Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

August 13, 2025
Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

August 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

August 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.