• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bauchi Ta Kori CSA Ibrahim Daga Aikin Gwamnati Kan Badakalarr Kudin Fansho

by Khalid Idris Doya
2 years ago
CSA Ibrahim

Gwamnatin Jihar Bauchi ta datse tare da kawo karshen aikin wani ma’aikacin gwamnati mai suna Ibrahim Garba da ke da matsayin babban mataimakin sakatare (CSA) bisa samunsa da laifin badakalarr kudade.

 

Ma’aikacin da aka kora ya na aiki ne da hukumar kula da fansho ta jihar an samesa ne da laifin handama da babakeren naira miliyan N3, 017, 919.30 mallakin wani dan fanshi da ya rigamu gidan gaskiya mai suna Audu Mohammed.

  • Kogon Hakar Ma’adinai Ya Kashe Mutum Hudu A Jihar Bauchi

A cewar sanarwar da jami’in watsa labarai na hukumar kula da ma’aikata ta jihar Bauchi (BSCSC), Malam Saleh Umar ya fitar a ranar Talata na cewa, “Ibrahim Garba dai, kwamitin ladabtarwa na hukumar fansho ya sameshi hannu dumu-dumu da yin wasu ‘yan dabarbaru wajen sauya asusun ajiyar bankin Abdu Mohammed wanda ya rigamu gidan gaskiya (Mamaci) da asusun ajiyarsa da hakan ya ba shi damar canza maballen sirri bayan da ahlin mamacin suka kai masa rahoton rasuwar Malam ‘Abdu’”.

 

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

Saleh Umar ya kara da cewa, hukumar ta amince da kawo karshen aikin Ibrahim Garba ne a yayin zamanta karo na 17 da aka gudanar a ranar 1 ga watan Agustan 2023.

 

Umar ya kara da cewa, “An samu jami’in da mummunar da’a ta hanyar shigar da kansa cikin badakalar albashi/fansho. Matakin nasa ya saba balo-balo wa tanade-tanaden dokokin aikin gwamnati (PSR) 0327(XI) da ta shafi almubazzarancin kudade.”

 

Sanarwar ta kara da cewa, “Ibrahim Garba ya amshi haramtaccen kudin fansho na watanni hamsin da biyar (55) da ya kai naira N54,871.26 kowace wata na tsawon shekaru hudu da watanni bakwai, sannan, adadin kudin da ya hamdame sun kai naira miliyan N3,017,919.30, kuma, kai tsaye za a kwatosu daga cikin hakkokinsa.”

 

Umar ya kuma nakalto shugaban hukumar kula da ma’aikata na jihar Bauchi, Alhaji Abubakar Usman Madakin Bunun Bauchi, da ya jagoranci zaman da aka gudanar wajen daukan wannan matakin, ya gargadi da jan kunnen ma’aikatan jihar da su kasance masu jin tsoron Allah da gudanar da aikinsu bisa da’a da bin dokoki da ka’idoji domin kauce wa shiga irin wannan matakin.

 

Shugaban ya ce, dole ne ma’aikata su kasance masu bin dokoki da ka’idojin aikin gwamnati domin tsarkakewa da tsaftace sashin aiki a kowani lokaci, ya na mai gargadin cewa duk wani ko wasu da aka kama da irin wannan ko makamancin wannan laifin tabbas zai fuskanci fushin hukumar ba makawa.

 

Ya bada tabbacin cewa, hukumar ba za ta zura ido tana kallo ko ta bari wasu bata-garin ma’aikata su kawo cikas ko bata kokarin gwamnati na kawo cigaba ga jihar musamman ta fuskacin kula da walwala da jin dadin aiki, sashin albashi da kuma biyan fansho.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
Manyan Labarai

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
Labarai

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Next Post
Gudu Zuwa Kasashen Waje: Gwamnati Na Shirin Taka Wa Likitoci Birki

Likitoci Masu Neman Kwarewa Sun Janye Zanga-zangar Da Suka Shirya

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.