ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bauchi Ta Kori CSA Ibrahim Daga Aikin Gwamnati Kan Badakalarr Kudin Fansho

by Khalid Idris Doya
3 years ago
CSA Ibrahim

Gwamnatin Jihar Bauchi ta datse tare da kawo karshen aikin wani ma’aikacin gwamnati mai suna Ibrahim Garba da ke da matsayin babban mataimakin sakatare (CSA) bisa samunsa da laifin badakalarr kudade.

 

Ma’aikacin da aka kora ya na aiki ne da hukumar kula da fansho ta jihar an samesa ne da laifin handama da babakeren naira miliyan N3, 017, 919.30 mallakin wani dan fanshi da ya rigamu gidan gaskiya mai suna Audu Mohammed.

ADVERTISEMENT
  • Kogon Hakar Ma’adinai Ya Kashe Mutum Hudu A Jihar Bauchi

A cewar sanarwar da jami’in watsa labarai na hukumar kula da ma’aikata ta jihar Bauchi (BSCSC), Malam Saleh Umar ya fitar a ranar Talata na cewa, “Ibrahim Garba dai, kwamitin ladabtarwa na hukumar fansho ya sameshi hannu dumu-dumu da yin wasu ‘yan dabarbaru wajen sauya asusun ajiyar bankin Abdu Mohammed wanda ya rigamu gidan gaskiya (Mamaci) da asusun ajiyarsa da hakan ya ba shi damar canza maballen sirri bayan da ahlin mamacin suka kai masa rahoton rasuwar Malam ‘Abdu’”.

 

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Saleh Umar ya kara da cewa, hukumar ta amince da kawo karshen aikin Ibrahim Garba ne a yayin zamanta karo na 17 da aka gudanar a ranar 1 ga watan Agustan 2023.

 

Umar ya kara da cewa, “An samu jami’in da mummunar da’a ta hanyar shigar da kansa cikin badakalar albashi/fansho. Matakin nasa ya saba balo-balo wa tanade-tanaden dokokin aikin gwamnati (PSR) 0327(XI) da ta shafi almubazzarancin kudade.”

 

Sanarwar ta kara da cewa, “Ibrahim Garba ya amshi haramtaccen kudin fansho na watanni hamsin da biyar (55) da ya kai naira N54,871.26 kowace wata na tsawon shekaru hudu da watanni bakwai, sannan, adadin kudin da ya hamdame sun kai naira miliyan N3,017,919.30, kuma, kai tsaye za a kwatosu daga cikin hakkokinsa.”

 

Umar ya kuma nakalto shugaban hukumar kula da ma’aikata na jihar Bauchi, Alhaji Abubakar Usman Madakin Bunun Bauchi, da ya jagoranci zaman da aka gudanar wajen daukan wannan matakin, ya gargadi da jan kunnen ma’aikatan jihar da su kasance masu jin tsoron Allah da gudanar da aikinsu bisa da’a da bin dokoki da ka’idoji domin kauce wa shiga irin wannan matakin.

 

Shugaban ya ce, dole ne ma’aikata su kasance masu bin dokoki da ka’idojin aikin gwamnati domin tsarkakewa da tsaftace sashin aiki a kowani lokaci, ya na mai gargadin cewa duk wani ko wasu da aka kama da irin wannan ko makamancin wannan laifin tabbas zai fuskanci fushin hukumar ba makawa.

 

Ya bada tabbacin cewa, hukumar ba za ta zura ido tana kallo ko ta bari wasu bata-garin ma’aikata su kawo cikas ko bata kokarin gwamnati na kawo cigaba ga jihar musamman ta fuskacin kula da walwala da jin dadin aiki, sashin albashi da kuma biyan fansho.

CSA Ibrahim
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
Next Post
Gudu Zuwa Kasashen Waje: Gwamnati Na Shirin Taka Wa Likitoci Birki

Likitoci Masu Neman Kwarewa Sun Janye Zanga-zangar Da Suka Shirya

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.