• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bauchi Ta Kori CSA Ibrahim Daga Aikin Gwamnati Kan Badakalarr Kudin Fansho

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Bauchi Ta Kori CSA Ibrahim Daga Aikin Gwamnati Kan Badakalarr Kudin Fansho
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Bauchi ta datse tare da kawo karshen aikin wani ma’aikacin gwamnati mai suna Ibrahim Garba da ke da matsayin babban mataimakin sakatare (CSA) bisa samunsa da laifin badakalarr kudade.

 

Ma’aikacin da aka kora ya na aiki ne da hukumar kula da fansho ta jihar an samesa ne da laifin handama da babakeren naira miliyan N3, 017, 919.30 mallakin wani dan fanshi da ya rigamu gidan gaskiya mai suna Audu Mohammed.

  • Kogon Hakar Ma’adinai Ya Kashe Mutum Hudu A Jihar Bauchi

A cewar sanarwar da jami’in watsa labarai na hukumar kula da ma’aikata ta jihar Bauchi (BSCSC), Malam Saleh Umar ya fitar a ranar Talata na cewa, “Ibrahim Garba dai, kwamitin ladabtarwa na hukumar fansho ya sameshi hannu dumu-dumu da yin wasu ‘yan dabarbaru wajen sauya asusun ajiyar bankin Abdu Mohammed wanda ya rigamu gidan gaskiya (Mamaci) da asusun ajiyarsa da hakan ya ba shi damar canza maballen sirri bayan da ahlin mamacin suka kai masa rahoton rasuwar Malam ‘Abdu’”.

 

Labarai Masu Nasaba

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

Saleh Umar ya kara da cewa, hukumar ta amince da kawo karshen aikin Ibrahim Garba ne a yayin zamanta karo na 17 da aka gudanar a ranar 1 ga watan Agustan 2023.

 

Umar ya kara da cewa, “An samu jami’in da mummunar da’a ta hanyar shigar da kansa cikin badakalar albashi/fansho. Matakin nasa ya saba balo-balo wa tanade-tanaden dokokin aikin gwamnati (PSR) 0327(XI) da ta shafi almubazzarancin kudade.”

 

Sanarwar ta kara da cewa, “Ibrahim Garba ya amshi haramtaccen kudin fansho na watanni hamsin da biyar (55) da ya kai naira N54,871.26 kowace wata na tsawon shekaru hudu da watanni bakwai, sannan, adadin kudin da ya hamdame sun kai naira miliyan N3,017,919.30, kuma, kai tsaye za a kwatosu daga cikin hakkokinsa.”

 

Umar ya kuma nakalto shugaban hukumar kula da ma’aikata na jihar Bauchi, Alhaji Abubakar Usman Madakin Bunun Bauchi, da ya jagoranci zaman da aka gudanar wajen daukan wannan matakin, ya gargadi da jan kunnen ma’aikatan jihar da su kasance masu jin tsoron Allah da gudanar da aikinsu bisa da’a da bin dokoki da ka’idoji domin kauce wa shiga irin wannan matakin.

 

Shugaban ya ce, dole ne ma’aikata su kasance masu bin dokoki da ka’idojin aikin gwamnati domin tsarkakewa da tsaftace sashin aiki a kowani lokaci, ya na mai gargadin cewa duk wani ko wasu da aka kama da irin wannan ko makamancin wannan laifin tabbas zai fuskanci fushin hukumar ba makawa.

 

Ya bada tabbacin cewa, hukumar ba za ta zura ido tana kallo ko ta bari wasu bata-garin ma’aikata su kawo cikas ko bata kokarin gwamnati na kawo cigaba ga jihar musamman ta fuskacin kula da walwala da jin dadin aiki, sashin albashi da kuma biyan fansho.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kudin fansho
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kakakin Ma’aikatar Wajen Sin Ya Yi Bayani Kan Taron Kasa Da Kasa Kan Batun Ukraine

Next Post

Likitoci Masu Neman Kwarewa Sun Janye Zanga-zangar Da Suka Shirya

Related

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya
Labarai

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

4 hours ago
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano
Labarai

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

5 hours ago
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari
Labarai

Za A Dinga Tunawa Da Buhari A Matsayin Waliyyi A Siyasar Nijeriya —Dakta Zangina

6 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

7 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas

7 hours ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

7 hours ago
Next Post
Gudu Zuwa Kasashen Waje: Gwamnati Na Shirin Taka Wa Likitoci Birki

Likitoci Masu Neman Kwarewa Sun Janye Zanga-zangar Da Suka Shirya

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.