• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Ya Kamata A Sani A Gasar Cin Kofin Afirka

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
Abubuwan Da Ya Kamata A Sani A Gasar Cin Kofin Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Kamar dai yadda hukumar kwallon kafa ta Nahiyar Turai ta bayyana, za a fara gasar ta cin kofin Afirka karo na 34 daga ranar 13 ga Janairu zuwa 11 ga watan Fabrairun 2024.

Karo na biyu ke nan da Ibory Coast za ta karbi bakuncin wasannin bayan na farko da ta karba a shekarar 1984 sai dai da farko, an tsara yin gasar daga watan Yuni zuwa Yulin shekara 2023 amma daga baya aka sauya wasannin saboda fargabar da ake da ita kan buga gasar a tsakiyar damuna.

  • Sin Za Ta Fadada Girman Tashar Binciken Samaniyarta
  • Gwamna Uba Sani Ya Taya Sarkin Zazzau Murnar Cika Shekara Uku A Kan Karagar Mulki 

Gasar za ta ci gaba da amsa takenta na 2023 duk kuwa da cewa za a buga ta ne a shekarar 2024 kuma wasan farko zai kunshi tawagar mai masaukin baki, wadda za ta fito cikin rukunin farko da za a hada ta da wasu tawagogin kasashe.

Kungiyoyin da suka yi na daya da na biyu a kowanne rukuni za su kai zagayen ‘yan 16, da wasu wadanda suka hada maki da yawa, amma suka kare a mataki na uku a rukuni daga shida da za a raba dauke da kasashe hudu kowanne – daga nan a buga wasan kusa da na kusa da na karshe da na dab da na karshe da karawar neman mataki na uku da kuma fafatawar karshe.

Filin wasa na Alassane Ouattara da ke Birnin Abidjan ne zai karbi bakuncin karawar karshe a ranar 11 ga watan Fabrairu, kamar yadda hukumar kwallon kafar Afirka CAF ta tabbatar.

Kusan wata daya za a kwashe ana fafatawa daga watan Janairu zuwa Fabrairu, inda fitattun ‘yan kwallo za su yi fatan lashe kofin babbar gasar kofin Afirka da hukumar CAF kan shirya.

Mai rike da kofin AFCON, Senegal za ta kira fitattun ‘yan kwallonta kamar Sadio Mane da ke wasa a Al-Nassr da na Chelsea, Nicolas Jackson, yayin da Masar, wadda ke kan gaba a yawan daukar kofin har karo bakwai – za ta kasance da kyaftin dinta mai buga wasa a Liberpool, Mohamed Salah.

Gasar ta wannan shekarar za ta kunshi kasashe 24, kuma a karo na uku, bayan an kara fadada wasanninta a 2019 kuma duk da yake Ibory Coast ce mai masaukin baki, amma ta buga wasannin neman shiga gasar, inda ta yi ta biyu a rukuni na takwas da Zambia ta ja ragama.

Kasashen biyu sun hade da 22 da suka yi na daya da na biyu a kowanne rukuni inda jimilla suka zama kasashe 24 domin fafatawa a wasannin da za a buga, sannan dukkan kasashen da za su je Ibory Coast sun fafata a gasar kofin Afirka biyu a baya, in ban da Zambia, wadda ta lashe gasar a 2012, kuma za ta buga gasar a karon farko bayan 2015 da kuma wadda za ta kara karo na biyar, rabonta da gasar dai tun a 2010.

Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya ta kusan shiga gasar a karon farko, amma ta barar da damar bayan ta yi rashin nasara a hannun Ghana, wadda ke sama da ita sai dai kasar Gabon ita ce fitacciyar kasa da ba za ta je gasar ba.

Za a raba jadawalin gasar ne a birnin Abidjan ranar 12 ga watan nan na Oktoba da karfe 7 na yamma agogon GMT, kuma za a yi la’akari da kwazon tawagogin a jerin gwanayen kasashen kwallon kafa da FIFA kan fitar, kuma kasashe 24 aka raba zuwa tukunya hudu.

Amma kuma Kasar Ibory Coast yanzu haka tana mataki na tara a kan gaba a kwallon kafa a Afirka, ita ma an saka ta a tukunyar raba rukuni saboda ita ce mai masaukin baki.

Yadda Za’a RabaJadawalin:

Tukunyar farko – Ibory Coast (50), Morocco (13), Senegal (20), Tunisia (29), Algeria (34), Egypt (35)

Tukunya ta biyu – Nigeria (40), Cameroon (41), Mali (49), Burkina Faso (58), Ghana (60), DR Congo (64)

Tukunya ta uku – South Africa (65), Cape Berde (71), Guinea (81), Zambia (82), Ekuatorial Guinea (92), Mauritania (99)

Tukunya ta hudu – Guinea-Bissau (106), Mozambikue (113), Namibia (114), Angola (117), The Gambia (118), Tanzania (122)

Za a raba kasashen zuwa rukuni shida da za su kunshi kasashe hurhudu kowanne, sannan kuma za a sanar da raneku da lokutan da za a fafata wasanni a Gasar ta AFCON 2023.

Filayen da za a buga wasannin:

Alassane Ouattara Stadium, Abidjan (Mai cin ‘yan kallo 60,000), Felid Houphouet Boigny Stadium, Abidjan (Mai cin ‘yan kallo 33,000) Stade de la Paid, Bouake (Mai cin ‘yan kallo 40,000) Amadou Gon Coulibaly Stadium, Korhogo (Mai cin ‘yan kallo 20,000)

Laurent Pokou Stadium, San Pedro (Mai cin ‘yan kallo 20,000) Charles Konan Banny Stadium, Yamoussoukro (Mai cin ‘yan kallo 20,000)

Hukumar kwallon kafa ta Afirka CAF na gayyatar fitattun ‘yan kwallon Nahiyar a lokacin da take gabatar da jadawalin kuma a wannan shekarar ma ana sa ran za a ga fitattun ‘yan wasan Ibory Coast, kamar Kolo Taure da dan uwansa Yaya Toure, wadanda suka buga wa kasar wasa, kuma suka doke Ghana kafin gasar a Kofi na biyu da Ibory Coast ta dauka a 2015.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Afirka Ta Kudu Sun Bayyana Dalilansu Na Kyamar Baki

Next Post

Dagwalon Nukiliyar Japan: Kar Duniya Ta Rungume Hannu Kilu Ta Ja Bau

Related

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu
Wasanni

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

18 hours ago
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan
Wasanni

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

21 hours ago
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal
Wasanni

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

21 hours ago
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona
Wasanni

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

3 days ago
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG
Wasanni

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

4 days ago
Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5
Wasanni

Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

6 days ago
Next Post
Dagwalon Nukiliyar Japan: Kar Duniya Ta Rungume Hannu Kilu Ta Ja Bau

Dagwalon Nukiliyar Japan: Kar Duniya Ta Rungume Hannu Kilu Ta Ja Bau

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.