• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Ya Kamata A Sani A Gasar Cin Kofin Afirka

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Kofin

LABARAI MASU NASABA

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Kamar dai yadda hukumar kwallon kafa ta Nahiyar Turai ta bayyana, za a fara gasar ta cin kofin Afirka karo na 34 daga ranar 13 ga Janairu zuwa 11 ga watan Fabrairun 2024.

Karo na biyu ke nan da Ibory Coast za ta karbi bakuncin wasannin bayan na farko da ta karba a shekarar 1984 sai dai da farko, an tsara yin gasar daga watan Yuni zuwa Yulin shekara 2023 amma daga baya aka sauya wasannin saboda fargabar da ake da ita kan buga gasar a tsakiyar damuna.

  • Sin Za Ta Fadada Girman Tashar Binciken Samaniyarta
  • Gwamna Uba Sani Ya Taya Sarkin Zazzau Murnar Cika Shekara Uku A Kan Karagar Mulki 

Gasar za ta ci gaba da amsa takenta na 2023 duk kuwa da cewa za a buga ta ne a shekarar 2024 kuma wasan farko zai kunshi tawagar mai masaukin baki, wadda za ta fito cikin rukunin farko da za a hada ta da wasu tawagogin kasashe.

Kungiyoyin da suka yi na daya da na biyu a kowanne rukuni za su kai zagayen ‘yan 16, da wasu wadanda suka hada maki da yawa, amma suka kare a mataki na uku a rukuni daga shida da za a raba dauke da kasashe hudu kowanne – daga nan a buga wasan kusa da na kusa da na karshe da na dab da na karshe da karawar neman mataki na uku da kuma fafatawar karshe.

Filin wasa na Alassane Ouattara da ke Birnin Abidjan ne zai karbi bakuncin karawar karshe a ranar 11 ga watan Fabrairu, kamar yadda hukumar kwallon kafar Afirka CAF ta tabbatar.

Kusan wata daya za a kwashe ana fafatawa daga watan Janairu zuwa Fabrairu, inda fitattun ‘yan kwallo za su yi fatan lashe kofin babbar gasar kofin Afirka da hukumar CAF kan shirya.

Mai rike da kofin AFCON, Senegal za ta kira fitattun ‘yan kwallonta kamar Sadio Mane da ke wasa a Al-Nassr da na Chelsea, Nicolas Jackson, yayin da Masar, wadda ke kan gaba a yawan daukar kofin har karo bakwai – za ta kasance da kyaftin dinta mai buga wasa a Liberpool, Mohamed Salah.

Gasar ta wannan shekarar za ta kunshi kasashe 24, kuma a karo na uku, bayan an kara fadada wasanninta a 2019 kuma duk da yake Ibory Coast ce mai masaukin baki, amma ta buga wasannin neman shiga gasar, inda ta yi ta biyu a rukuni na takwas da Zambia ta ja ragama.

Kasashen biyu sun hade da 22 da suka yi na daya da na biyu a kowanne rukuni inda jimilla suka zama kasashe 24 domin fafatawa a wasannin da za a buga, sannan dukkan kasashen da za su je Ibory Coast sun fafata a gasar kofin Afirka biyu a baya, in ban da Zambia, wadda ta lashe gasar a 2012, kuma za ta buga gasar a karon farko bayan 2015 da kuma wadda za ta kara karo na biyar, rabonta da gasar dai tun a 2010.

Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya ta kusan shiga gasar a karon farko, amma ta barar da damar bayan ta yi rashin nasara a hannun Ghana, wadda ke sama da ita sai dai kasar Gabon ita ce fitacciyar kasa da ba za ta je gasar ba.

Za a raba jadawalin gasar ne a birnin Abidjan ranar 12 ga watan nan na Oktoba da karfe 7 na yamma agogon GMT, kuma za a yi la’akari da kwazon tawagogin a jerin gwanayen kasashen kwallon kafa da FIFA kan fitar, kuma kasashe 24 aka raba zuwa tukunya hudu.

Amma kuma Kasar Ibory Coast yanzu haka tana mataki na tara a kan gaba a kwallon kafa a Afirka, ita ma an saka ta a tukunyar raba rukuni saboda ita ce mai masaukin baki.

Yadda Za’a RabaJadawalin:

Tukunyar farko – Ibory Coast (50), Morocco (13), Senegal (20), Tunisia (29), Algeria (34), Egypt (35)

Tukunya ta biyu – Nigeria (40), Cameroon (41), Mali (49), Burkina Faso (58), Ghana (60), DR Congo (64)

Tukunya ta uku – South Africa (65), Cape Berde (71), Guinea (81), Zambia (82), Ekuatorial Guinea (92), Mauritania (99)

Tukunya ta hudu – Guinea-Bissau (106), Mozambikue (113), Namibia (114), Angola (117), The Gambia (118), Tanzania (122)

Za a raba kasashen zuwa rukuni shida da za su kunshi kasashe hurhudu kowanne, sannan kuma za a sanar da raneku da lokutan da za a fafata wasanni a Gasar ta AFCON 2023.

Filayen da za a buga wasannin:

Alassane Ouattara Stadium, Abidjan (Mai cin ‘yan kallo 60,000), Felid Houphouet Boigny Stadium, Abidjan (Mai cin ‘yan kallo 33,000) Stade de la Paid, Bouake (Mai cin ‘yan kallo 40,000) Amadou Gon Coulibaly Stadium, Korhogo (Mai cin ‘yan kallo 20,000)

Laurent Pokou Stadium, San Pedro (Mai cin ‘yan kallo 20,000) Charles Konan Banny Stadium, Yamoussoukro (Mai cin ‘yan kallo 20,000)

Hukumar kwallon kafa ta Afirka CAF na gayyatar fitattun ‘yan kwallon Nahiyar a lokacin da take gabatar da jadawalin kuma a wannan shekarar ma ana sa ran za a ga fitattun ‘yan wasan Ibory Coast, kamar Kolo Taure da dan uwansa Yaya Toure, wadanda suka buga wa kasar wasa, kuma suka doke Ghana kafin gasar a Kofi na biyu da Ibory Coast ta dauka a 2015.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
Wasanni

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara
Wasanni

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
Wasanni

Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

November 2, 2025
Next Post
Dagwalon Nukiliyar Japan: Kar Duniya Ta Rungume Hannu Kilu Ta Ja Bau

Dagwalon Nukiliyar Japan: Kar Duniya Ta Rungume Hannu Kilu Ta Ja Bau

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025
Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.