ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Ya Kamata A Sani A Gasar Cin Kofin Afirka

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Kofin

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

Kamar dai yadda hukumar kwallon kafa ta Nahiyar Turai ta bayyana, za a fara gasar ta cin kofin Afirka karo na 34 daga ranar 13 ga Janairu zuwa 11 ga watan Fabrairun 2024.

Karo na biyu ke nan da Ibory Coast za ta karbi bakuncin wasannin bayan na farko da ta karba a shekarar 1984 sai dai da farko, an tsara yin gasar daga watan Yuni zuwa Yulin shekara 2023 amma daga baya aka sauya wasannin saboda fargabar da ake da ita kan buga gasar a tsakiyar damuna.

  • Sin Za Ta Fadada Girman Tashar Binciken Samaniyarta
  • Gwamna Uba Sani Ya Taya Sarkin Zazzau Murnar Cika Shekara Uku A Kan Karagar Mulki 

Gasar za ta ci gaba da amsa takenta na 2023 duk kuwa da cewa za a buga ta ne a shekarar 2024 kuma wasan farko zai kunshi tawagar mai masaukin baki, wadda za ta fito cikin rukunin farko da za a hada ta da wasu tawagogin kasashe.

Kungiyoyin da suka yi na daya da na biyu a kowanne rukuni za su kai zagayen ‘yan 16, da wasu wadanda suka hada maki da yawa, amma suka kare a mataki na uku a rukuni daga shida da za a raba dauke da kasashe hudu kowanne – daga nan a buga wasan kusa da na kusa da na karshe da na dab da na karshe da karawar neman mataki na uku da kuma fafatawar karshe.

Filin wasa na Alassane Ouattara da ke Birnin Abidjan ne zai karbi bakuncin karawar karshe a ranar 11 ga watan Fabrairu, kamar yadda hukumar kwallon kafar Afirka CAF ta tabbatar.

Kusan wata daya za a kwashe ana fafatawa daga watan Janairu zuwa Fabrairu, inda fitattun ‘yan kwallo za su yi fatan lashe kofin babbar gasar kofin Afirka da hukumar CAF kan shirya.

Mai rike da kofin AFCON, Senegal za ta kira fitattun ‘yan kwallonta kamar Sadio Mane da ke wasa a Al-Nassr da na Chelsea, Nicolas Jackson, yayin da Masar, wadda ke kan gaba a yawan daukar kofin har karo bakwai – za ta kasance da kyaftin dinta mai buga wasa a Liberpool, Mohamed Salah.

Gasar ta wannan shekarar za ta kunshi kasashe 24, kuma a karo na uku, bayan an kara fadada wasanninta a 2019 kuma duk da yake Ibory Coast ce mai masaukin baki, amma ta buga wasannin neman shiga gasar, inda ta yi ta biyu a rukuni na takwas da Zambia ta ja ragama.

Kasashen biyu sun hade da 22 da suka yi na daya da na biyu a kowanne rukuni inda jimilla suka zama kasashe 24 domin fafatawa a wasannin da za a buga, sannan dukkan kasashen da za su je Ibory Coast sun fafata a gasar kofin Afirka biyu a baya, in ban da Zambia, wadda ta lashe gasar a 2012, kuma za ta buga gasar a karon farko bayan 2015 da kuma wadda za ta kara karo na biyar, rabonta da gasar dai tun a 2010.

Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya ta kusan shiga gasar a karon farko, amma ta barar da damar bayan ta yi rashin nasara a hannun Ghana, wadda ke sama da ita sai dai kasar Gabon ita ce fitacciyar kasa da ba za ta je gasar ba.

Za a raba jadawalin gasar ne a birnin Abidjan ranar 12 ga watan nan na Oktoba da karfe 7 na yamma agogon GMT, kuma za a yi la’akari da kwazon tawagogin a jerin gwanayen kasashen kwallon kafa da FIFA kan fitar, kuma kasashe 24 aka raba zuwa tukunya hudu.

Amma kuma Kasar Ibory Coast yanzu haka tana mataki na tara a kan gaba a kwallon kafa a Afirka, ita ma an saka ta a tukunyar raba rukuni saboda ita ce mai masaukin baki.

Yadda Za’a RabaJadawalin:

Tukunyar farko – Ibory Coast (50), Morocco (13), Senegal (20), Tunisia (29), Algeria (34), Egypt (35)

Tukunya ta biyu – Nigeria (40), Cameroon (41), Mali (49), Burkina Faso (58), Ghana (60), DR Congo (64)

Tukunya ta uku – South Africa (65), Cape Berde (71), Guinea (81), Zambia (82), Ekuatorial Guinea (92), Mauritania (99)

Tukunya ta hudu – Guinea-Bissau (106), Mozambikue (113), Namibia (114), Angola (117), The Gambia (118), Tanzania (122)

Za a raba kasashen zuwa rukuni shida da za su kunshi kasashe hurhudu kowanne, sannan kuma za a sanar da raneku da lokutan da za a fafata wasanni a Gasar ta AFCON 2023.

Filayen da za a buga wasannin:

Alassane Ouattara Stadium, Abidjan (Mai cin ‘yan kallo 60,000), Felid Houphouet Boigny Stadium, Abidjan (Mai cin ‘yan kallo 33,000) Stade de la Paid, Bouake (Mai cin ‘yan kallo 40,000) Amadou Gon Coulibaly Stadium, Korhogo (Mai cin ‘yan kallo 20,000)

Laurent Pokou Stadium, San Pedro (Mai cin ‘yan kallo 20,000) Charles Konan Banny Stadium, Yamoussoukro (Mai cin ‘yan kallo 20,000)

Hukumar kwallon kafa ta Afirka CAF na gayyatar fitattun ‘yan kwallon Nahiyar a lokacin da take gabatar da jadawalin kuma a wannan shekarar ma ana sa ran za a ga fitattun ‘yan wasan Ibory Coast, kamar Kolo Taure da dan uwansa Yaya Toure, wadanda suka buga wa kasar wasa, kuma suka doke Ghana kafin gasar a Kofi na biyu da Ibory Coast ta dauka a 2015.

Kofin
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
Wasanni

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Next Post
Dagwalon Nukiliyar Japan: Kar Duniya Ta Rungume Hannu Kilu Ta Ja Bau

Dagwalon Nukiliyar Japan: Kar Duniya Ta Rungume Hannu Kilu Ta Ja Bau

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.