• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nasihar Kwankwaso Ga Angwaye Da Amaren Kano: Ku Guji Binciken Wayoyin Junanku

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Nasihar Kwankwaso Ga Angwaye Da Amaren Kano: Ku Guji Binciken Wayoyin Junanku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wata nasiha kuma gargaɗi da jan-kunne, tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya shawarci ma’aurata 1,500 da aka ɗaura wa auren zawarawa a Kano cewa, kada su maida hankali wajen binciken wayoyin junansu.

Kwankwaso wanda shi ne madugun Kwankwasiyya kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na NNPP a zaɓen 2023, ya ce yawan binciken wayoyi da ma’aurata ke yi ne sahun gaba wajen yawan rabuwar aure.

  • Zaben Kano: Ba Mu Yarda A Karya ‘Yancin Dimokuradiyya Ba – Kungiya
  • ‘Yansanda Sun Cafke Mutum 3 Bisa Zargin Fashi Da Makami A Jihar Kano

Kwankwaso ya yi wannan nasihar ce a ranar Juma’a, wurin walimar da Gwamnatin Jihar Kano ta shirya wa Angwayen da Amaren a dandalin taro na Gidan Gwamnatin Kano, a ranar Asabar.

Tun da farko, a ranar Juma’a, Gwamna Abba Yusuf ne ya tsaya a matsayin waliyyin auren zawarawan, wanda aka gudanar lokaci ɗaya a faɗin ƙananan hukumomi 44 da ke Jihar Kano.

An shirya ɗaura aure 1,800 a lokaci ɗaya, amma kuma an samu ma’aurata 300 da lamarin bai yiwu ba, saboda dalilai na rashin lafiya.

Labarai Masu Nasaba

NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA

“Na tabbata ana ta ba ku shawarwari daban-daban da nasihohi da gargaɗi kusan kila sau dubu. Malamai, iyaye da danginku da ma ‘yan kasuwa duk sun sha ba ku shawarwarin yadda za ku yi zaman aure a cikin kwanciyar hankali.

“To amma dai ni ina da wata shawara ɗaya, wato kada ku riƙa leƙe-leƙen binciken wayoyin junanku, domin yin hakan ya kawo sanadiyyar mutuwar aure da yawa,” inji Kwankwaso.

Daga nan ya yaba da irin namijin ƙoƙarin da Gwamnan Kano Abba Yusuf ya yi wajen shirya wannan gagarimin bikin auren dandazon zawarawa a Kano.

Haka kuma ya yaba wa Gwamnatin Kano dangane da kashe Naira miliyan 700 wajen ɗaukar nauyin ɗalibai 600 zuwa karatu jami’o’i daban-daban a ƙasashen waje.

A na sa jawabin, Gwamna Abba ya ce Gwamnatin Jihar Kano ce ta ɗauki nauyin shirya auren, ita ta biya sadakin kowane ango da kuma kayan ɗakin amarya, har da kayan gara na kayan abinci da kuma tallafin Naira 20,000 ga kowace amarya domin ta samu jarin fara sana’ar rage raɗaɗin tsadar rayuwa a gidajen auren su.

Daga nan ya hore su su yi zaman lafiya da juna a bisa tafarkin Musulunci.

Gwamna Abba ya ce, an zaɓo ma’auratan ne 30 daga kowace ƙaramar hukuma ɗaya, daga cikin ƙananan hukumomi 44 da jihar ke da su.

A jawabin sa, Shugaban Hukumar Hisbah, Aminu Daurawa, ya ce an ɗaura aure 1,500 a ranar Juma’a.

Ya ce waɗanda ba a samu damar ɗaura auren na su ba saboda lalurar rashin lafiya, su 264 ne, kuma za a ɗaura auren na su da zarar sun kammala shan magani nan gaba kaɗan.

Daurawa ya yi masu nasiha da su sa tsoron Allah a zamantakewar aure a tsakanin su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AureAuren zawarawa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Layin Dogo Mai Saurin Tafiya Tsakanin Jakarta Da Bandung Na Indonesiya

Next Post

Magoya Bayan Kasar Ingila Sun Yi Wa Henderson Ihu A Wasansu Da Australia

Related

NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya
Labarai

NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

6 minutes ago
Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA
Labarai

Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA

1 hour ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

2 hours ago
Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

3 hours ago
Ba A Taɓa Nuno Bidiyon Shugaban Jam’iyyarmu Ta ADC Yana Cusa Dala A Aljihu Ba —Dalung
Labarai

Ba A Taɓa Nuno Bidiyon Shugaban Jam’iyyarmu Ta ADC Yana Cusa Dala A Aljihu Ba —Dalung

3 hours ago
Ayyukan ‘Yan Ta’adda Na Barazana Ga Shirin Gwamnati Na Wadata Kasa Da Abinci
Labarai

Ayyukan ‘Yan Ta’adda Na Barazana Ga Shirin Gwamnati Na Wadata Kasa Da Abinci

5 hours ago
Next Post
Magoya Bayan Kasar Ingila Sun Yi Wa Henderson Ihu A Wasansu Da Australia

Magoya Bayan Kasar Ingila Sun Yi Wa Henderson Ihu A Wasansu Da Australia

LABARAI MASU NASABA

NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

July 4, 2025
Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA

Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA

July 4, 2025
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

July 4, 2025

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

July 4, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

July 4, 2025
Ba A Taɓa Nuno Bidiyon Shugaban Jam’iyyarmu Ta ADC Yana Cusa Dala A Aljihu Ba —Dalung

Ba A Taɓa Nuno Bidiyon Shugaban Jam’iyyarmu Ta ADC Yana Cusa Dala A Aljihu Ba —Dalung

July 4, 2025
Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (1)

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (1)

July 4, 2025
Ayyukan ‘Yan Ta’adda Na Barazana Ga Shirin Gwamnati Na Wadata Kasa Da Abinci

Ayyukan ‘Yan Ta’adda Na Barazana Ga Shirin Gwamnati Na Wadata Kasa Da Abinci

July 4, 2025
Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

July 4, 2025
‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

July 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.