ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karbar Haraji Mai Yawa Ne Ya Durkusar Da Masana’antu A Nijeriya – Kwamiti

by Sadiq
2 years ago
Haraji

Kwamitin shugaban kasa kan inganta karbar haraji da dokokin kudi ya shawarci gwamnatin Nijeriya da ta zabtare wasu jerin haraji har 190 da ake karba daga hannun talakawan kasar nan.

Wannan dai ta zama wata hanya da za a bi wajen sakarwa masu kamfanonin da masana’antu mara, ta yadda za su samu damar gudanar da ayyukansu da kuma samun riba cikin sauki.

  • Kotun Koli Ta Tsayar Da Ranar Alhamis Don Yanke Hukunci Kan Zaben Shugaban Kasa
  • Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Fika Ya Rasu Yana Da Shekara 90

A cikin wani rahoto bayan bincike da kwamitin ya gabatar wa shugaba Tinubu, ya zargi jihohi da karbar harajin da ya wuce kima, kuma bisa rashin ka’ida.

ADVERTISEMENT

Rahoton kwamitin ya ce wannan harajin barkatai da jihohi ke karba, shi ne sanadin tashin farashin kayayyaki da rashin samun ribar da ta dace da kuma lalacewar darajar Naira da sauran matsaloli.

Kwamitin ya yi misali da korafin da kamfanonin sadarwa suka jima suna yi game da yadda jihohi suka mayar da su saniyar tatsa ta yadda suke karbar jerin haraji.

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Yayin da yake gabatar da korafin kamfanonin sadarwar, shugaban kungiyar kamfanonin, Gbolahan Awonuga ya ce kowanne kamfanin sadarwa yana biyan haraji daban-daban har guda 40 ko sama da haka duk wata, abin da ya ce yana haddasa musu karancin abokan ciniki saboda tsada.

Shugaban kwamitin shugaban kasa Mista Taiwo Oyedele ya ce kwamitin na shawartar gwamnatin tarayya ta hade haraji fiye da 200 daban-daban da masu kamfanoni ke biya zuwa 10.

Kwamitin ya kuma bukaci gwamnatin tarayya ta yi gaggawar mayar da hankalin kan fannin tattalin arziki, don shawo kan matsalar hauhawar farashin kayayyaki da kuma lalacewar darajar Naira.

Ana ci gaba da kokawa kan yadda farashin kayan masarufi ke yin tashin gwauron zabi, lamarin da ya sanya dubban mutane gaza cin abinci sau uku a rana.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Gwamnan Jihar California Dake Amurka

Xi Jinping Ya Gana Da Gwamnan Jihar California Dake Amurka

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.