ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar ‘One Germany’ Ta Fara Gangamin Samar Da Karin Masu Zuba Jari A Afirika

by Bello Hamza
2 years ago
One

Hadin gwiwa da kungiyar ‘ONE Germany’ zai bunkasa shigowar masu zuba jari nahiyar Afirika, kungiyar ta bayyana haka ne a takardar sanarwa da aka raba wa manema labarai a kan ziyarar da Shugaban kasa Jamus, Olaf Scholz, ya kawo Nijeriya da Ghana daga ranar Lahadi da ta gabata.

Kungiyar ta yi kira na musamman ga shugaban kasar na Jamus da ya samar da yanayi da zai karfafa ‘yan kasuwar kasar Jamus don su shigo su zuba jari a bangarori daban-daban na tattalin arzikin nahiyar Afirika.

  • Yadda Na Sha Mugun Duka A Hannun ‘Yansanda — Ajaero
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Kebbi Ta Samu Sabon Shugaba

Daraktan kungiyar ta ‘ONE Germany’, Stephan Edo-Kreischer, ya kara da cewa, “Yadda Shugaba Scholz ya dauki zuba jari a nahiyar Afirka da muhimmancin gaske, abu ne da ya kamata duk dan kasar Jamus ya yaba da matakin, musamman ganin zuba jari a Afirka tamka karfafa tattalin arzikkn kasa Jamus ne, a kan haka bai kamata a bari wannan kokari ya zama furuci na siyasa ba kawai.

ADVERTISEMENT

“An dade kasashen da suka ci gaba a Turai suna watsi da Afirka, a kan haka wasu kasashe ke komawa wasu kasashe kamar Chana, yanzu lokaci ya yi da za a karfafa danganta da Afirka don gudanar da hulda mai amfanar da juna.

“Wannan kuma yana zuwa ne a daidai lokacin da Afirika ke tsananin bukatar karin jari don bunkasa bangarorin tattalin arziki da dama. Afirka na bukatar a ji muryarta fiye da duk wani lokaci a baya.”

LABARAI MASU NASABA

Danyen Mai Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Zuwa Ganga Miliyan 1.436 —OPEC

An Jinjina Wa Tinubu Bisa Mayar Da Ofishin Ayyukan NPA Garin Warri

Daraktan kungiyar a Nijeriya, Stanley Achonu, ya ce shugaban kasar Jamus, Scholz ya jagoranci kiran kara zuba jari a Afirka a kuma shigo da Afirka a cikin manyan kungiyoyin bunkasa tattalin arziki na duniya.

Achonu ya kuma kara da cewa, “Shuugaba Scholz ya jagoranci kiran a tabbatar da shigo ga Afirka a cikin tafiyar kungiyar G20, wanda kuma tuni a aka sanya Afirka a taron da aka gudanar kwanan nan. Amma lallai wannan bai isa ba, dole Afirka ta samu wakilci a manyan cibiyoyin kudi na duniya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Danyen Mai Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Zuwa Ganga Miliyan 1.436 —OPEC
Tattalin Arziki

Danyen Mai Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Zuwa Ganga Miliyan 1.436 —OPEC

December 19, 2025
An Jinjina Wa Tinubu Bisa Mayar Da Ofishin Ayyukan NPA Garin Warri
Tattalin Arziki

An Jinjina Wa Tinubu Bisa Mayar Da Ofishin Ayyukan NPA Garin Warri

December 19, 2025
Annabi SAW Ya Zarce Duk Sauran Annabawa Yawan Mu’uzijoji
Tattalin Arziki

Gwamna Radda Ya Dora Harsashin Gina Ma’aikatar Sarrafa Rogo A Katsina

December 13, 2025
Next Post
Sojoji Sun Ceto Masu Yi Wa Kasa Hidima 2 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Katsina

Sojoji Sun Ceto Masu Yi Wa Kasa Hidima 2 Daga Hannun 'Yan Bindiga A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.