• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abarbar Benin Ta Shaida Yadda Kasar Sin Ke Kara Bude Kofarta

by CGTN Hausa
2 years ago
Benin

Wani abokina ya taba zuwa kasar Benin yau da shekaru da suka wuce, bayan da ya dawo gida, ya kan tuna da abarbar kasar ta Benin mai dadin gaske.

A kwanakin da suka wuce, abokin nawa ya yi matukar farin ciki, inda ya gaya min cewa, an amince a shigo da abarbar kasar Benin kasuwar kasar Sin, don haka ma zai samu damar dandana su a gida ba tare da yin doguwar tafiya har zuwa Benin ba.

  • Dandalin Hongqiao Na Maida Hankali Ga Kiyaye Tsarin Cinikayyar Sassa Daban Daban
  • CIIE Na Da Matukar Muhimmanci Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Abarba na daga cikin muhimman nau’o’in amfanin gona da ake samarwa a kasar Benin, wanda ake mata kirarin “Burodi mai zaki na Afirka”, sakamakon irin dandanonta na musamman. A yayin da shugaban kasar Benin ya kawo ziyara kasar Sin a watan Satumban bana, kasashen biyu sun daddale yarjejeniya game da shigowa da abarbar kasar Benin cikin kasuwar kasar Sin.

Watanni biyu kacal, an fara ganin abarbar Benin a gun bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin (CIIE) karo na shida da yanzu haka ke gudana a birnin Shanghai da ke gabashin kasar Sin, wadda ta yi matukar janyo hankalin al’umma. A game da wannan, jakadan kasar Benin a kasar Sin, Simon Pierre Adovelande ya bayyana cewa, “ina fatan masu sayayya na kasar Sin za su kara fahimtar abarba mai dadi ta Benin, kuma muna fatan samun ’yan kasuwar kasar Sin da za su kai abarbarmu zuwa kasuwar kasar, har ma da teburin al’ummar Sinawa.”

A cikin ’yan shekarun baya, kasar Sin ta yi ta sa kaimin shigowa da kayayyaki masu inganci na kasa da kasa, don duniya ta more babbar kasuwarta da ma ci gabanta. Abin lura shi ne, kasar Sin ta bullo da wata kafar musamman ta shigowa da amfanin gona na kasashen Afirka, don tallafawa kasashen Afirka wajen fitar da karin amfanin gonarsu. Avokado na Kenya da barkono na Ruwanda da Lemo na Afirka ta Kudu da wake na Tanzania, har ma da Abarba na Benin, na daga cikin karin kayayyakin kasashen Afirka da suka samu damar shiga babbar kasuwar kasar Sin, wadanda a sa’i daya suka kyautata rayuwar al’ummar Sinawa, a sa’i dayan kuma, suka taimaka ga ci gaban tattalin arzikin kasashen da suke fitar da kayayyakinsu.

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

Bana ake cika shekaru 45 da kasar Sin ta fara aiwatar da manufar yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga ketare, kana shekaru 10 da Sin din ta gabatar da shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”, haka kuma shekara ta shida da kasar ta shirya bikin baje kolin kayayyaki da ake shigowa da su kasar Sin, bikin da ya kasance irinsa na farko a duniya da ke mai da hankali musamman a kan kayayyakin da ake shigowa da su daga ketare. A yayin da farfadowar kariyar ciniki da ra’ayin cacar baka ke haifar da barazana ga dunkulewar tattalin arzikin duniya, yadda kasar Sin ke tsayawa tsayin daka a kan bude kofarta ga ketare, da ma kawar da shingen ciniki tare da kasashen da suka karbi shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”, ya shaida niyyarta wajen ganin an tabbatar da ci gaban bai daya na kasa da kasa, haka kuma ya bayyana ma’anar “Gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ga dukkanin bil Adam” da ta gabatar. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025
An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal
Daga Birnin Sin

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025
Daga Birnin Sin

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
Next Post
Kwayoyi

Za Mu Karfafa Yaki Da Miyagun Kwayoyi A Jihar Zamfara - Gwamna Lawal 

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025
An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

October 10, 2025
Nijeriya

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

October 10, 2025
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

October 10, 2025
Benin

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.