• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abarbar Benin Ta Shaida Yadda Kasar Sin Ke Kara Bude Kofarta

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Abarbar Benin Ta Shaida Yadda Kasar Sin Ke Kara Bude Kofarta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani abokina ya taba zuwa kasar Benin yau da shekaru da suka wuce, bayan da ya dawo gida, ya kan tuna da abarbar kasar ta Benin mai dadin gaske.

A kwanakin da suka wuce, abokin nawa ya yi matukar farin ciki, inda ya gaya min cewa, an amince a shigo da abarbar kasar Benin kasuwar kasar Sin, don haka ma zai samu damar dandana su a gida ba tare da yin doguwar tafiya har zuwa Benin ba.

  • Dandalin Hongqiao Na Maida Hankali Ga Kiyaye Tsarin Cinikayyar Sassa Daban Daban
  • CIIE Na Da Matukar Muhimmanci Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Abarba na daga cikin muhimman nau’o’in amfanin gona da ake samarwa a kasar Benin, wanda ake mata kirarin “Burodi mai zaki na Afirka”, sakamakon irin dandanonta na musamman. A yayin da shugaban kasar Benin ya kawo ziyara kasar Sin a watan Satumban bana, kasashen biyu sun daddale yarjejeniya game da shigowa da abarbar kasar Benin cikin kasuwar kasar Sin.

Watanni biyu kacal, an fara ganin abarbar Benin a gun bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin (CIIE) karo na shida da yanzu haka ke gudana a birnin Shanghai da ke gabashin kasar Sin, wadda ta yi matukar janyo hankalin al’umma. A game da wannan, jakadan kasar Benin a kasar Sin, Simon Pierre Adovelande ya bayyana cewa, “ina fatan masu sayayya na kasar Sin za su kara fahimtar abarba mai dadi ta Benin, kuma muna fatan samun ’yan kasuwar kasar Sin da za su kai abarbarmu zuwa kasuwar kasar, har ma da teburin al’ummar Sinawa.”

A cikin ’yan shekarun baya, kasar Sin ta yi ta sa kaimin shigowa da kayayyaki masu inganci na kasa da kasa, don duniya ta more babbar kasuwarta da ma ci gabanta. Abin lura shi ne, kasar Sin ta bullo da wata kafar musamman ta shigowa da amfanin gona na kasashen Afirka, don tallafawa kasashen Afirka wajen fitar da karin amfanin gonarsu. Avokado na Kenya da barkono na Ruwanda da Lemo na Afirka ta Kudu da wake na Tanzania, har ma da Abarba na Benin, na daga cikin karin kayayyakin kasashen Afirka da suka samu damar shiga babbar kasuwar kasar Sin, wadanda a sa’i daya suka kyautata rayuwar al’ummar Sinawa, a sa’i dayan kuma, suka taimaka ga ci gaban tattalin arzikin kasashen da suke fitar da kayayyakinsu.

Labarai Masu Nasaba

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Bana ake cika shekaru 45 da kasar Sin ta fara aiwatar da manufar yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga ketare, kana shekaru 10 da Sin din ta gabatar da shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”, haka kuma shekara ta shida da kasar ta shirya bikin baje kolin kayayyaki da ake shigowa da su kasar Sin, bikin da ya kasance irinsa na farko a duniya da ke mai da hankali musamman a kan kayayyakin da ake shigowa da su daga ketare. A yayin da farfadowar kariyar ciniki da ra’ayin cacar baka ke haifar da barazana ga dunkulewar tattalin arzikin duniya, yadda kasar Sin ke tsayawa tsayin daka a kan bude kofarta ga ketare, da ma kawar da shingen ciniki tare da kasashen da suka karbi shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”, ya shaida niyyarta wajen ganin an tabbatar da ci gaban bai daya na kasa da kasa, haka kuma ya bayyana ma’anar “Gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ga dukkanin bil Adam” da ta gabatar. (Mai Zane:Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaSinTattalin Arziki
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Fitar Da Gargadin Zubar Dusar Kankara Da Iskar Hunturu A Sassan Arewa Maso Gabashin Kasar Sin

Next Post

Za Mu Karfafa Yaki Da Miyagun Kwayoyi A Jihar Zamfara – Gwamna Lawal 

Related

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
Daga Birnin Sin

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

6 hours ago
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

7 hours ago
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 
Daga Birnin Sin

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

8 hours ago
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika
Daga Birnin Sin

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

9 hours ago
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150
Daga Birnin Sin

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

10 hours ago
Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

1 day ago
Next Post
Kwayoyi

Za Mu Karfafa Yaki Da Miyagun Kwayoyi A Jihar Zamfara - Gwamna Lawal 

LABARAI MASU NASABA

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

August 9, 2025
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

August 9, 2025
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.