• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,127, Sun Sace 518 A Watan Oktoba – Rahoto

by Sadiq
2 years ago
Rahoto

Wani rahoton tsaro na wata-wata da wani kamfani mai zaman kansa na tsaro, Beacon Consulting Ltd ya fitar, ya ce a Nijeriya an samu rahotannin tsaro 935, inda mutane 1,127 suka mutu a hannun ‘yan bindiga a watan Oktoba, 2023.

Rahoton da aka fitar a ranar 15 ga watan Nuwamba, 2023, ya ce an yi garkuwa da mutane 518 a tsawon lokacin, yayin da matsalar tsaro ta kara ta’azzara idan aka kwatanta da watannin baya.

  • Nijeriya Za Ta Bayar Da Fifiko Ga Fasaha Da Makamashi Shettima
  • Yadda Za A Sake Farawa Daga Birnin San Francisco

Rahoton ya yi nazari ne kan al’amuran tsaro da suka faru a Nijeriya daga tsakanin 1 zuwa 31 ga watan Oktoban 2023.

A cewar rahoton, a watan Oktoban 2023, “Nijeriya ta fuskanci matsalolin tsaro 935 wanda ke nuni da karuwar kashi 70.6 cikin 100 daga bayanan da aka fitar a watan Satumba; an samu asarar rayuka 1,127 wanda ke nuni da karuwar kashi 93.97 cikin 100, sannan an sace mutane 518 da ke wakiltar kashi 50.6 cikin 100.”

Rahoton ya kuma yi nuni da cewa yankin Arewa-maso-Gabas ne ya fi kowane yankin yawan fuskantar matsalar tsaro da asarar rayuka, da kuma sace-sacen jama’a, yayin da yankin Arewa-maso-maso-Yamma ke bi masa baya.

LABARAI MASU NASABA

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

Bayanai daga cibiyar tsaro ta Beacon sun nuna cewa an samu bayanan matsalar tsaro 466, kazalika an samu asarar rayuka 433, da kuma sace mutane 253 a fadin kananan hukumomi 62 da ke yankin Arewa maso Gabashin Nijeriya.

“Rikicin tsakanin ISWAP) da Jama’atu Ahlis Sunna Lidda’awati wal Jihad (JAS) ya taimaka wajen karuwar adadin.”

Rahoton ya kara da cewa an samu asarar rayuka a yankin Arewa maso Gabas.

Manajan daraktan kamfanin Beacon Consulting Limited, Dokta Kabir Adamu, ya yi karin haske game da rahoton, inda ya bayyana matsalolin rashin tsaro a Nijeriya da kuma bukatar yin amfani da tsarin da bayanan da kamfanin Beacon Consulting ke fitarwa domin inganta rayuwar daidaikun mutane da tsaron kasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Next Post
An Kafa Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje 41,947 A Kasar Sin Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

An Kafa Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje 41,947 A Kasar Sin Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

October 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

October 14, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

PDP Ta Ɗage Babban Taronta Biyo Bayan Ficewar Wasu Manyan Jiga-jigai

October 14, 2025
An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

October 14, 2025
Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

October 14, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

October 14, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

October 14, 2025
Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

October 14, 2025
Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

October 13, 2025
Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.