ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,127, Sun Sace 518 A Watan Oktoba – Rahoto

by Sadiq
3 years ago
Rahoto

Wani rahoton tsaro na wata-wata da wani kamfani mai zaman kansa na tsaro, Beacon Consulting Ltd ya fitar, ya ce a Nijeriya an samu rahotannin tsaro 935, inda mutane 1,127 suka mutu a hannun ‘yan bindiga a watan Oktoba, 2023.

Rahoton da aka fitar a ranar 15 ga watan Nuwamba, 2023, ya ce an yi garkuwa da mutane 518 a tsawon lokacin, yayin da matsalar tsaro ta kara ta’azzara idan aka kwatanta da watannin baya.

  • Nijeriya Za Ta Bayar Da Fifiko Ga Fasaha Da Makamashi Shettima
  • Yadda Za A Sake Farawa Daga Birnin San Francisco

Rahoton ya yi nazari ne kan al’amuran tsaro da suka faru a Nijeriya daga tsakanin 1 zuwa 31 ga watan Oktoban 2023.

ADVERTISEMENT

A cewar rahoton, a watan Oktoban 2023, “Nijeriya ta fuskanci matsalolin tsaro 935 wanda ke nuni da karuwar kashi 70.6 cikin 100 daga bayanan da aka fitar a watan Satumba; an samu asarar rayuka 1,127 wanda ke nuni da karuwar kashi 93.97 cikin 100, sannan an sace mutane 518 da ke wakiltar kashi 50.6 cikin 100.”

Rahoton ya kuma yi nuni da cewa yankin Arewa-maso-Gabas ne ya fi kowane yankin yawan fuskantar matsalar tsaro da asarar rayuka, da kuma sace-sacen jama’a, yayin da yankin Arewa-maso-maso-Yamma ke bi masa baya.

LABARAI MASU NASABA

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

Bayanai daga cibiyar tsaro ta Beacon sun nuna cewa an samu bayanan matsalar tsaro 466, kazalika an samu asarar rayuka 433, da kuma sace mutane 253 a fadin kananan hukumomi 62 da ke yankin Arewa maso Gabashin Nijeriya.

“Rikicin tsakanin ISWAP) da Jama’atu Ahlis Sunna Lidda’awati wal Jihad (JAS) ya taimaka wajen karuwar adadin.”

Rahoton ya kara da cewa an samu asarar rayuka a yankin Arewa maso Gabas.

Manajan daraktan kamfanin Beacon Consulting Limited, Dokta Kabir Adamu, ya yi karin haske game da rahoton, inda ya bayyana matsalolin rashin tsaro a Nijeriya da kuma bukatar yin amfani da tsarin da bayanan da kamfanin Beacon Consulting ke fitarwa domin inganta rayuwar daidaikun mutane da tsaron kasa.

MASU ALAKA

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Umarnin Kawo Karshen Matsalar Tsaro
Rahotonni

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

September 5, 2026
Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
Rahotonni

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

September 5, 2026
Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
Rahotonni

Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki

September 5, 2026
Next Post
An Kafa Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje 41,947 A Kasar Sin Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

An Kafa Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje 41,947 A Kasar Sin Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.