• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Za Ta Zaftare Kudaden Kananan Hukumomin Da Ba A Yi Zabe Ba

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Sabbin Ministoci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rikicin tsarin mulki ya kunno kai yayin da Majalisar Dattawan Nijeriya ta zartas da wani kuduri na neman Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu ya hana wa kananan hukumomin da ba su zabi shugabanni ba kudadensu.

Sai dai kudurin majalisar dattawan ya saba wa hukunce-hukuncen kotun koli, inda ta bayyana cewa shugaban kasa ba shi da hurumin hana kudaden da ake ware wa jihohi da kananan hukumomi.

  • Za A Shiga Mummunar Damuwa A Gaza Idan Ba Ku Dauki Mataki Ba – Gargadi Ga Majalisar Tsaro Ta MDD
  • Badakala: Majalisar Wakilai Ta Bayar Da Umurnin Cafke Gwamnan CBN, Babban Akanta Na Kasa Da Sauransu 

Tuni dai kudurin ya fuskanci suka na ganin yadda ‘yan majalisar ke kokarin yin adawa da hukuncin kotun koli.

Akwai jihohi da dama da ba su gudanar da zaben kananan hukumomi ba, inda kantomomin ne ke jan ragamar tafiyar da kananan hukumomin.

A wani taron zaman majalisan, ‘yan majalisar dattawan sun bukaci Shugaba Tinubu ya rike kudaden kananan hukumomin da ba su yi zaben shugabannin kananan hukumomi da kansiloli ba.

Labarai Masu Nasaba

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

Hakan ya biyo bayan kudurin da shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa, Abba Moro ya gabatar wanda ya koka da gazawar wasu gwamnatocin jihohi wajen gudanar da zaben kananan hukumomi.

Bisa gabatar da wannan kuduri ne majalisar dattawan ta bukaci bangaren zartarwa da ta hana wa kananan hukumomin da ba za a zaba ba kudadensu.

Kudurin ya yi Allah wadai da rusa zaben shugabannin kananan hukumomin a Benuwai da sauran jihohin Nijeriya.

Ya bukaci gwamnan Jihar Benuwai da ya kiyaye rantsuwar da ya yi na yin biyayya ga doka da kuma kare kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya.

Kudurin majalisar dattawan ya yi kira da gwamnan ya sake yin nazari a kan rusa zababbun shugabannin kananan hukumomi tare da dawo da su nan take.

Sanata Abba Moro, mai wakiltar Benuwai ta Kudu wanda shi ne shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa ya ce ya damu matuka kan rusa zababbun shugabannin kananan hukumomi da kansilolin da aka yi a Jihar Benuwai.

Da yake bayar da gudunmuwarsa a kan muhawarar, Sanata Adams Oshiomhole mai wakiltar Edo ta Arewa ya ce a halin yanzu kusan jihohi 16 a Nijeriya ba su da zababbun shugabannin wadanda aka zaba ta hanyar dimokuradiyya.

Ya ce ya kamata majalisar dattawa ta umurci ministan kudi ya dakatar da bayar da kudade ga kananan hukumomin da ba su da zababbun shugabannin da kansiloli. Shawarar ta kuma samu goyon bayan babban mai tsawatarwa na majalisar dattawa, Sanata Ali Ndume.

Har ila yau, Sanata Abdulfatai Buhari da ke wakiltar Oyo ta Arewa ya tabo wani batu na daban, ya ce kamata ya yi a gyara dokar zabe ta yadda za a bai wa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) damar gudanar da zaben kananan hukumom


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Albashin ma'aikataKananan HukumomiSanatoci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Katsina Ta Kara Jaddada Matsayinta Kan Bunkasa Ilimi

Next Post

Tinubu Zai Sake Fuskantar Wata Shari’ar A Kotun Koli Kan Zaben 2023

Related

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

6 days ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

1 month ago
Next Post
Tinubu

Tinubu Zai Sake Fuskantar Wata Shari’ar A Kotun Koli Kan Zaben 2023

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.