ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Za Ta Zaftare Kudaden Kananan Hukumomin Da Ba A Yi Zabe Ba

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Sabbin Ministoci

Rikicin tsarin mulki ya kunno kai yayin da Majalisar Dattawan Nijeriya ta zartas da wani kuduri na neman Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu ya hana wa kananan hukumomin da ba su zabi shugabanni ba kudadensu.

Sai dai kudurin majalisar dattawan ya saba wa hukunce-hukuncen kotun koli, inda ta bayyana cewa shugaban kasa ba shi da hurumin hana kudaden da ake ware wa jihohi da kananan hukumomi.

  • Za A Shiga Mummunar Damuwa A Gaza Idan Ba Ku Dauki Mataki Ba – Gargadi Ga Majalisar Tsaro Ta MDD
  • Badakala: Majalisar Wakilai Ta Bayar Da Umurnin Cafke Gwamnan CBN, Babban Akanta Na Kasa Da Sauransu 

Tuni dai kudurin ya fuskanci suka na ganin yadda ‘yan majalisar ke kokarin yin adawa da hukuncin kotun koli.

ADVERTISEMENT

Akwai jihohi da dama da ba su gudanar da zaben kananan hukumomi ba, inda kantomomin ne ke jan ragamar tafiyar da kananan hukumomin.

A wani taron zaman majalisan, ‘yan majalisar dattawan sun bukaci Shugaba Tinubu ya rike kudaden kananan hukumomin da ba su yi zaben shugabannin kananan hukumomi da kansiloli ba.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Hakan ya biyo bayan kudurin da shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa, Abba Moro ya gabatar wanda ya koka da gazawar wasu gwamnatocin jihohi wajen gudanar da zaben kananan hukumomi.

Bisa gabatar da wannan kuduri ne majalisar dattawan ta bukaci bangaren zartarwa da ta hana wa kananan hukumomin da ba za a zaba ba kudadensu.

Kudurin ya yi Allah wadai da rusa zaben shugabannin kananan hukumomin a Benuwai da sauran jihohin Nijeriya.

Ya bukaci gwamnan Jihar Benuwai da ya kiyaye rantsuwar da ya yi na yin biyayya ga doka da kuma kare kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya.

Kudurin majalisar dattawan ya yi kira da gwamnan ya sake yin nazari a kan rusa zababbun shugabannin kananan hukumomi tare da dawo da su nan take.

Sanata Abba Moro, mai wakiltar Benuwai ta Kudu wanda shi ne shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa ya ce ya damu matuka kan rusa zababbun shugabannin kananan hukumomi da kansilolin da aka yi a Jihar Benuwai.

Da yake bayar da gudunmuwarsa a kan muhawarar, Sanata Adams Oshiomhole mai wakiltar Edo ta Arewa ya ce a halin yanzu kusan jihohi 16 a Nijeriya ba su da zababbun shugabannin wadanda aka zaba ta hanyar dimokuradiyya.

Ya ce ya kamata majalisar dattawa ta umurci ministan kudi ya dakatar da bayar da kudade ga kananan hukumomin da ba su da zababbun shugabannin da kansiloli. Shawarar ta kuma samu goyon bayan babban mai tsawatarwa na majalisar dattawa, Sanata Ali Ndume.

Har ila yau, Sanata Abdulfatai Buhari da ke wakiltar Oyo ta Arewa ya tabo wani batu na daban, ya ce kamata ya yi a gyara dokar zabe ta yadda za a bai wa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) damar gudanar da zaben kananan hukumom

majalisar Dattawa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Tinubu

Tinubu Zai Sake Fuskantar Wata Shari’ar A Kotun Koli Kan Zaben 2023

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.