ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Za Ta Zaftare Kudaden Kananan Hukumomin Da Ba A Yi Zabe Ba

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Sabbin Ministoci

Rikicin tsarin mulki ya kunno kai yayin da Majalisar Dattawan Nijeriya ta zartas da wani kuduri na neman Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu ya hana wa kananan hukumomin da ba su zabi shugabanni ba kudadensu.

Sai dai kudurin majalisar dattawan ya saba wa hukunce-hukuncen kotun koli, inda ta bayyana cewa shugaban kasa ba shi da hurumin hana kudaden da ake ware wa jihohi da kananan hukumomi.

  • Za A Shiga Mummunar Damuwa A Gaza Idan Ba Ku Dauki Mataki Ba – Gargadi Ga Majalisar Tsaro Ta MDD
  • Badakala: Majalisar Wakilai Ta Bayar Da Umurnin Cafke Gwamnan CBN, Babban Akanta Na Kasa Da Sauransu 

Tuni dai kudurin ya fuskanci suka na ganin yadda ‘yan majalisar ke kokarin yin adawa da hukuncin kotun koli.

ADVERTISEMENT

Akwai jihohi da dama da ba su gudanar da zaben kananan hukumomi ba, inda kantomomin ne ke jan ragamar tafiyar da kananan hukumomin.

A wani taron zaman majalisan, ‘yan majalisar dattawan sun bukaci Shugaba Tinubu ya rike kudaden kananan hukumomin da ba su yi zaben shugabannin kananan hukumomi da kansiloli ba.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Hakan ya biyo bayan kudurin da shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa, Abba Moro ya gabatar wanda ya koka da gazawar wasu gwamnatocin jihohi wajen gudanar da zaben kananan hukumomi.

Bisa gabatar da wannan kuduri ne majalisar dattawan ta bukaci bangaren zartarwa da ta hana wa kananan hukumomin da ba za a zaba ba kudadensu.

Kudurin ya yi Allah wadai da rusa zaben shugabannin kananan hukumomin a Benuwai da sauran jihohin Nijeriya.

Ya bukaci gwamnan Jihar Benuwai da ya kiyaye rantsuwar da ya yi na yin biyayya ga doka da kuma kare kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya.

Kudurin majalisar dattawan ya yi kira da gwamnan ya sake yin nazari a kan rusa zababbun shugabannin kananan hukumomi tare da dawo da su nan take.

Sanata Abba Moro, mai wakiltar Benuwai ta Kudu wanda shi ne shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa ya ce ya damu matuka kan rusa zababbun shugabannin kananan hukumomi da kansilolin da aka yi a Jihar Benuwai.

Da yake bayar da gudunmuwarsa a kan muhawarar, Sanata Adams Oshiomhole mai wakiltar Edo ta Arewa ya ce a halin yanzu kusan jihohi 16 a Nijeriya ba su da zababbun shugabannin wadanda aka zaba ta hanyar dimokuradiyya.

Ya ce ya kamata majalisar dattawa ta umurci ministan kudi ya dakatar da bayar da kudade ga kananan hukumomin da ba su da zababbun shugabannin da kansiloli. Shawarar ta kuma samu goyon bayan babban mai tsawatarwa na majalisar dattawa, Sanata Ali Ndume.

Har ila yau, Sanata Abdulfatai Buhari da ke wakiltar Oyo ta Arewa ya tabo wani batu na daban, ya ce kamata ya yi a gyara dokar zabe ta yadda za a bai wa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) damar gudanar da zaben kananan hukumom

majalisar Dattawa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Tinubu

Tinubu Zai Sake Fuskantar Wata Shari’ar A Kotun Koli Kan Zaben 2023

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.