ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Za Ta Zaftare Kudaden Kananan Hukumomin Da Ba A Yi Zabe Ba

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Sabbin Ministoci

Rikicin tsarin mulki ya kunno kai yayin da Majalisar Dattawan Nijeriya ta zartas da wani kuduri na neman Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu ya hana wa kananan hukumomin da ba su zabi shugabanni ba kudadensu.

Sai dai kudurin majalisar dattawan ya saba wa hukunce-hukuncen kotun koli, inda ta bayyana cewa shugaban kasa ba shi da hurumin hana kudaden da ake ware wa jihohi da kananan hukumomi.

  • Za A Shiga Mummunar Damuwa A Gaza Idan Ba Ku Dauki Mataki Ba – Gargadi Ga Majalisar Tsaro Ta MDD
  • Badakala: Majalisar Wakilai Ta Bayar Da Umurnin Cafke Gwamnan CBN, Babban Akanta Na Kasa Da Sauransu 

Tuni dai kudurin ya fuskanci suka na ganin yadda ‘yan majalisar ke kokarin yin adawa da hukuncin kotun koli.

ADVERTISEMENT

Akwai jihohi da dama da ba su gudanar da zaben kananan hukumomi ba, inda kantomomin ne ke jan ragamar tafiyar da kananan hukumomin.

A wani taron zaman majalisan, ‘yan majalisar dattawan sun bukaci Shugaba Tinubu ya rike kudaden kananan hukumomin da ba su yi zaben shugabannin kananan hukumomi da kansiloli ba.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

Hakan ya biyo bayan kudurin da shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa, Abba Moro ya gabatar wanda ya koka da gazawar wasu gwamnatocin jihohi wajen gudanar da zaben kananan hukumomi.

Bisa gabatar da wannan kuduri ne majalisar dattawan ta bukaci bangaren zartarwa da ta hana wa kananan hukumomin da ba za a zaba ba kudadensu.

Kudurin ya yi Allah wadai da rusa zaben shugabannin kananan hukumomin a Benuwai da sauran jihohin Nijeriya.

Ya bukaci gwamnan Jihar Benuwai da ya kiyaye rantsuwar da ya yi na yin biyayya ga doka da kuma kare kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya.

Kudurin majalisar dattawan ya yi kira da gwamnan ya sake yin nazari a kan rusa zababbun shugabannin kananan hukumomi tare da dawo da su nan take.

Sanata Abba Moro, mai wakiltar Benuwai ta Kudu wanda shi ne shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa ya ce ya damu matuka kan rusa zababbun shugabannin kananan hukumomi da kansilolin da aka yi a Jihar Benuwai.

Da yake bayar da gudunmuwarsa a kan muhawarar, Sanata Adams Oshiomhole mai wakiltar Edo ta Arewa ya ce a halin yanzu kusan jihohi 16 a Nijeriya ba su da zababbun shugabannin wadanda aka zaba ta hanyar dimokuradiyya.

Ya ce ya kamata majalisar dattawa ta umurci ministan kudi ya dakatar da bayar da kudade ga kananan hukumomin da ba su da zababbun shugabannin da kansiloli. Shawarar ta kuma samu goyon bayan babban mai tsawatarwa na majalisar dattawa, Sanata Ali Ndume.

Har ila yau, Sanata Abdulfatai Buhari da ke wakiltar Oyo ta Arewa ya tabo wani batu na daban, ya ce kamata ya yi a gyara dokar zabe ta yadda za a bai wa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) damar gudanar da zaben kananan hukumom

majalisar Dattawa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Tinubu

Tinubu Zai Sake Fuskantar Wata Shari’ar A Kotun Koli Kan Zaben 2023

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.