• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kawancen Yakar APC: Jam’iyyun Adawa Sun Shiga Dimuwa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
APC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ga dukkan alamu yunkurin da jam’iyyun adawa ke yi na yin kawance domin yakar jam’iyya mai Mulki ta APC ya shiga garari, yayin da wasu manyan jam’iyyun adawa suka nesanta kansu da lamarin.

A ranar Alhamis 7 ga Disambar 2023, wasu rahotanni sun yi nuni da cewa akwai wasu jam’iyyun adawa su 7 da suke kokarin yin kawancen siyasa domin fatattakar jam’iyyar APC daga kan maragar mulkin Nijeriya.
Gamayyar jam’iyyun sun kunshi PDP da ADC da SDP da PAM da NNPP da YPP da kuma ZLP.

  • Ministan Wajen Angola: Manyan Ababen More Rayuwa Da Kamfanonin Sin Suka Gina A Kasar Angola Sun Inganta Ci Gaban Kasar

Taron hadin kan sun yi ne da nufin yakar jam’iyya mai mulki ta APC, wanda rahotanni ya nuna cewa shugabannin jam’iyyun ne suka yi wannan taron a babban hedikwatan jam’iyyar SDP da ke Abuja.

Shugaban jam’iyyar SDP na kasa, Shehu Gabam ya ce jam’iyyun sun gaji matuka kan yadda yanayin kasar nan yake a birkice, babu wani abu da ke tafiya daidai, musamman yadda ake samun rudani a shari’u da aka yi na gwamnoni kanar a jihohin Zamfara da Nasarawa da Kano da Filato.

Jami’iyyun adawa dai sun yi rashin nasara a kotuna a wadannan jihohin bayan da hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ta ayyanasu a matsayin wadanda suka yi nasara.
Bayanai dai na nuna cewa babbar jam’iyyar adawa a Najeriya ta PDP ta sami wakilci a taron, inda mai rikon mukamin sakataren jam’iyyar na kasa, Senonji Koshedo ya wakilci mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, Umar Damagum.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

A cewar shugabannin jam’iyyun adawar dai, babban dalilin wannan hadin kan shi ne a tabbatar da ingancin dimokuradiyya a Nijeriya ta hanayar samun jam’iyyar adawa mai karfin gaske da za ta iya tunkarar jam’iyya mai mulki.

Amma kuma wasu bayanai na nuna cewa kawancen da aka yi bai kai ga yin maja ba, ma’ana jam’iyyun siyasar za su kasance a matsayinsu na jam’iyyu masu zaman kansu ko da za su yi aiki tare don kawar da APC.
Ko da yake wasu na ganin cewa wannan kawance nasu ba mai yiwuwa ba ne don kowa manufarsa daban. Sanin kowa ne sai hali ya zo daya ake abota.

Haka kuma wasu bayanan na nuna cewa wasu wakilan jam’iyyun da suka halarci taron sun je ne a karin kansu ba da yawun jam’iyyunsu ba.
Duk da yake mai rikon sakataren jam’iyyar PDP na kasa, Koshoedo ya halarci taron ya kuma nuna goyon bayansa a taron, amma jam’iyyar PDP ta nesanta kanta da hadin gwiwar. Sakataren watsa labaran PDP, Debo Ologunagba, ya musanta shiga tattaunawar yin kawance da jam’iyyun adawan guda shida.

Ita ma a nata bangaren, kwamitin gudanarwa na jam’iyyar NNPP ya nesanta kansa da shiga tattaunawar kawance da wasu jam’iyyun adawa. Jam’iyyar NNPP ta kasa ta bayyana haka ne a wata sanarwa da mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, Abba Ali, ya fitar a birnin tarayya Abuja. Ya ce NNPP ba ta daga cikin mambobin gamayyar jam’iyyun da suka cure wuri daya domin yin kawance.

Sanarwar ta ce, “An jawo hankalin shugabancin jam’iyya kan wasu rahotannin da jaridu suka wallafa cewa an kafa gamayyar jam’iyyu kuma ta kunshi NNPP da wasu jam’iyyun siyasa.”
“Muna mai farin cikin sanar da cewa babu wani abu makamancin haka. Rahoton wanda ya watsu ranar Jumu’a, 8 ga watan Satumba, 2023 ya nuna cewa NNPP, PDP da wasu jam’iyyu sun yi kawance.”

Ali ya kara da cewa tun bayan zaben 2023, babu wani mamban NNPP da ya zauna da wata jam’iyya ko tawaga ko daidaiku da nufin tattaunawar kawance.

Jam’iyyar LP sun barranta kansu da shiga wannan hadaka kamar yadda mai magana da yawun jam’iyyar, Obiora Ifoh ya bayyana. Ya ce ba da su ba, don ba a kama hanyar hadin kai ba. ya ce idan za su yi hadaka za su duba tanaje-tanajen dokokin zabe da ya samar a kan hadaka.

Alamu dai na nuna cewa gamayyar jam’iyyun adawa ba su tsara ainihin yadda za a yi hadakar ba, duk da yake sakataren hadakar jam’iyyun, Willy Ezugwu ya ce hadakarsu na jam’iyyu masu rajista a Nijeriya ne, don haka ba suna karkashin wani ba ne da za su amsa sunansa.

Abun da kowa zai duba shi ne, hannu daya ba ya daukan jinka, kuma idan ana neman samun nasara a kowani abu dole ne a hadu waje guda don a sami nasarar, kamar abun da ya faru a shekarar 2014 inda jam’iyyun adawa suka hadu suka kafa jam’iyyar APC wanda ta sami nasara a zaben shekarar 2015.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCLPPDP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Kungiyar USCBC

Next Post

Gwamnonin Arewa Sun Bada Tallafin Naira Miliyan 180 Ga Al’ummar Tudun biri

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

4 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Gwamnonin Arewa Sun Bada Tallafin Naira Miliyan 180 Ga Al’ummar Tudun biri

Gwamnonin Arewa Sun Bada Tallafin Naira Miliyan 180 Ga Al'ummar Tudun biri

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.