• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamoti B Laori Ya Kaddamar Da Ajujuwa 3 A Mazabar Kodomti A Numan

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
in Labarai
0
Kwamoti B Laori Ya Kaddamar Da Ajujuwa 3 A Mazabar Kodomti A Numan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kokarin da yake yi na inganta harkar ilmi da ababen more rayuwa a mazabarsa, dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Demsa/Numan/Lamurde a majalisar tarayya ya kaddamar da rukunin ajujuwa 3 a unguwar Kodomti da ke karamar hukumar Numan.

Da yake jawabi a ranar Laraba a wajen taron, dan majalisar ya koka kan matsalar karancin ababen more rayuwa a mafi yawan al’ummar mazabar, inda ya jaddada kudirinsa na ganin an inganta ilimi a lokacin mulkinsa.

  • Kotu Ta Raba Auren Shekaru 7 Saboda Rashin Soyayya
  • Wata Mata Ta Sace Jariri Sabuwar Haihuwa A Asibiti A Nasarawa

Dan majalisar ya bayyana cewa ingantaccen yanayin koyon karatu yana da muhimmanci ga rayuwar yara, don gudanar da ingantaccen koyo.

Bayan bayar da tallafin karatu ga dalibai a matakai daban-daban na ilimi, ya jaddada cewa tare da ilimi ya zo da ‘yanci, tare da yin alkawarin kara tsoma baki a fannin.

Kwamoti

Labarai Masu Nasaba

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Dan majalisar ya yi amfani da wannan damar wajen nuna godiya ga irin goyon bayan da ya samu daga jama’ar mazabarsa tare da yin alkawarin ba zai taba bata ba su kunya ba.

Al’ummar mazabar Kodomti karkashin jagorancin su Ndewodi Kodomti da Ha Shaforon, sun cika da farin cikin bisa kaddamar da ginin ajujuwa.

Kwamoti

Jama’a da dama sun fito don nuna godiya ga dan majalisar, sun yi addu’ar Allah ya taimaki dan majalisar ya samu nasara a duk kokarin da yake aikin inganta rayuwar al’ummar mazabarsa.

Al’ummar Kodomti ta yi fice wajen noma da kamun kifi, sun gabatar da kyautar kifi katann guda ga dan majalisar, a matsayin alamar kauna da godiya.

Abubuwan da suka fi daukar hankali a taron sun hada da gabatar da al’adu da al’ummar Kodomti da Bandawa suka nuna.

Kwamoti

A nasu bangaren, daliban makarantar firamare ta Kodomti sun gabatar da jawabai da dama cikin wakoki da kasidu domin nuna godiya ga dan majalisar tarayyar.

Cikin manyan bakin da suka halarci bikin sun hada da Ndewodi Kodomti, Ha Shaforon, Hon. Pwamwakaino Makondo, shugabannin kananan hukumomin Numan da Lamurde.

Shugabannin jam’iyyarsa da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP a Numan, Demsa Lamurde duk sun halarci taro.

Kwamoti

Haka kuma dan majalisa Kwamoti B La’ori, ya ziyarci kasuwar Numan, domin jajanta wa ‘yan kasuwar da iftila’in gobara ya kone musu shaguna kurmus.

Ya yi fatan Allah ya tsayar da lamarin haka, sannan ya yi alkawarin tallafa musu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AjujuwaDan MajalisaIlimiNuman
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Satar Jariri A Nasarawa

Next Post

Sin Na Fatan Taimakawa Ghana Kan Matsalar Basusukan Da Ake Bin Ta

Related

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

54 minutes ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

4 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

5 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

15 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

17 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

19 hours ago
Next Post
Sin Na Fatan Taimakawa Ghana Kan Matsalar Basusukan Da Ake Bin Ta

Sin Na Fatan Taimakawa Ghana Kan Matsalar Basusukan Da Ake Bin Ta

LABARAI MASU NASABA

Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.