• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sake Fasalin Naira Ya Taimaka Wajen Samun  Ingantaccen Zabe A 2023 —Buhari Ya Jaddada

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Dole A Hada Karfi Wajen Dakile Bazuwar Makamai A Afirka –Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya bayyana cewa sauya fasalin naira ya yi matukar taimaka wa wajen samar da ingataccen zabe a 2023.

Ya kuma bayyana dalilin da ya sa bai kori tsohon gwamnan babban bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele duk da an alakanta shi da neman tikitin takarar shugaban kasa a APC a 2023.

  • Jihar Kaduna Za Ta Ƙarfafa Ƙawancen Tattalin Arziki Da Ƙasar Jamus
  • Sin Ta Riga Ta Bayar Da Gudunmawar Da Ake Bukata Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

A cewarsa, ba zai iya korar Emefiele daga ofis ba saboda bai fada masa burinsa ba na neman shugaban Nijeriya ba.

Buhari ya bayyana hakan ne a wurin kaddamar da littafin ayyukan da ya yi tun daga 2015 zuwa 2023, wanda tsohon mai magana da yawunsa, Femi Adesina ya rubuta.

An dai kaddamar da littafin ne a hukumance a Abuja ranar Talata, Buhari ya kare manufar sake fasalin naira da Emefiele ya aiwatar, inda ya tabbatar da cewa ta taimaka wajen samar da ingantaccen zabe a 2023.

Labarai Masu Nasaba

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

Tsohon shugaban kasar ya ci gaba da cewa wadanda ke da matsala da manufar sake fasalin naira mutane ne da ke da kudade masu yawa.

Buhari ya ce, “Ba da gangan muka sauya fasanin naira ba da kuma samun karancin kudade da aka yi domin hukunta ‘yan Nijeriya ba. Dimokuradiyya tana ba mutane damar bayyana ra’ayinsu, kuma ba mu yi kokarin hana su ba. Mutane sun fahimci illar bin ra’ayinsu a zaben, kuma ba mu tilasta musu ba.

“Jihata ta Katsina an samu kyakkyawan tsari. A zaben shugaban kasa, APC ta sha kaye. Amma ta samu nasara a zaben gwamna. Watakila sun yi sakaci ne saboda suna tunanin ita ce jihata, kuma suna tunanin za su yi nasara cikin sauki. Mutane ba sa son a yi sakaci wajen gudanar da zabe domin haka zai sa a sha mamaki.

“Na sami Emefiele a ofis a lokacin da na zo a matsayin shugaban kasa, ban samu wasu kwararan hujjoji a kansa da sa in sallame shi daga matsayinsa na gwamnan CBN.

“Idan ka azabtar da mutum bisa zalunci, ba zai iya mantawa ba har tsawon rayuwarsa, don haka idan za ka hukunta mutum, dole ne ka sami kwararen hujjoji. Kuma ya kamata ka sani cewa ba za ka tabbtar a mukami ba har abada. Dole ne wata rana sai ka bar wannan mukamin da kake.

“Lokacin da aka alakanta shi da neman takaran shugaban kasa a 2023, ban tambaye shi ba, saboda bai fada wa kowa ba cewa yana da muradin zama shugaban kasa. In ba haka ba, da na cire shi tare da yi wa al’umma bayanin dalilin da ya sa.

“Babu shakka manufar sake fasalin naira ta ba mu zabuka mai matukar tsafta. Mutanen da ke da makudan kudade ne suka sami matsala da tsarin,” in ji Buhari.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mahalartan WEF: Sin Muhimmiyar Injin Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa

Next Post

Ziyarar Ministan Wajen Sin A Afirka: Zumunci Mai Dadi Ba Irin Na ’Yan Ta-more Ba

Related

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

4 days ago
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

2 weeks ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

2 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 month ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 month ago
Next Post
Ziyarar Ministan Wajen Sin A Afirka: Zumunci Mai Dadi Ba Irin Na ’Yan Ta-more Ba

Ziyarar Ministan Wajen Sin A Afirka: Zumunci Mai Dadi Ba Irin Na ’Yan Ta-more Ba

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

August 27, 2025
Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.