ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sake Fasalin Naira Ya Taimaka Wajen Samun  Ingantaccen Zabe A 2023 —Buhari Ya Jaddada

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Naira

Tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya bayyana cewa sauya fasalin naira ya yi matukar taimaka wa wajen samar da ingataccen zabe a 2023.

Ya kuma bayyana dalilin da ya sa bai kori tsohon gwamnan babban bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele duk da an alakanta shi da neman tikitin takarar shugaban kasa a APC a 2023.

  • Jihar Kaduna Za Ta Ƙarfafa Ƙawancen Tattalin Arziki Da Ƙasar Jamus
  • Sin Ta Riga Ta Bayar Da Gudunmawar Da Ake Bukata Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

A cewarsa, ba zai iya korar Emefiele daga ofis ba saboda bai fada masa burinsa ba na neman shugaban Nijeriya ba.

ADVERTISEMENT

Buhari ya bayyana hakan ne a wurin kaddamar da littafin ayyukan da ya yi tun daga 2015 zuwa 2023, wanda tsohon mai magana da yawunsa, Femi Adesina ya rubuta.

An dai kaddamar da littafin ne a hukumance a Abuja ranar Talata, Buhari ya kare manufar sake fasalin naira da Emefiele ya aiwatar, inda ya tabbatar da cewa ta taimaka wajen samar da ingantaccen zabe a 2023.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Tsohon shugaban kasar ya ci gaba da cewa wadanda ke da matsala da manufar sake fasalin naira mutane ne da ke da kudade masu yawa.

Buhari ya ce, “Ba da gangan muka sauya fasanin naira ba da kuma samun karancin kudade da aka yi domin hukunta ‘yan Nijeriya ba. Dimokuradiyya tana ba mutane damar bayyana ra’ayinsu, kuma ba mu yi kokarin hana su ba. Mutane sun fahimci illar bin ra’ayinsu a zaben, kuma ba mu tilasta musu ba.

“Jihata ta Katsina an samu kyakkyawan tsari. A zaben shugaban kasa, APC ta sha kaye. Amma ta samu nasara a zaben gwamna. Watakila sun yi sakaci ne saboda suna tunanin ita ce jihata, kuma suna tunanin za su yi nasara cikin sauki. Mutane ba sa son a yi sakaci wajen gudanar da zabe domin haka zai sa a sha mamaki.

“Na sami Emefiele a ofis a lokacin da na zo a matsayin shugaban kasa, ban samu wasu kwararan hujjoji a kansa da sa in sallame shi daga matsayinsa na gwamnan CBN.

“Idan ka azabtar da mutum bisa zalunci, ba zai iya mantawa ba har tsawon rayuwarsa, don haka idan za ka hukunta mutum, dole ne ka sami kwararen hujjoji. Kuma ya kamata ka sani cewa ba za ka tabbtar a mukami ba har abada. Dole ne wata rana sai ka bar wannan mukamin da kake.

“Lokacin da aka alakanta shi da neman takaran shugaban kasa a 2023, ban tambaye shi ba, saboda bai fada wa kowa ba cewa yana da muradin zama shugaban kasa. In ba haka ba, da na cire shi tare da yi wa al’umma bayanin dalilin da ya sa.

“Babu shakka manufar sake fasalin naira ta ba mu zabuka mai matukar tsafta. Mutanen da ke da makudan kudade ne suka sami matsala da tsarin,” in ji Buhari.

Naira
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

MASU ALAKA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
Next Post
Ziyarar Ministan Wajen Sin A Afirka: Zumunci Mai Dadi Ba Irin Na ’Yan Ta-more Ba

Ziyarar Ministan Wajen Sin A Afirka: Zumunci Mai Dadi Ba Irin Na ’Yan Ta-more Ba

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.