ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sake Fasalin Naira Ya Taimaka Wajen Samun  Ingantaccen Zabe A 2023 —Buhari Ya Jaddada

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Naira

Tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya bayyana cewa sauya fasalin naira ya yi matukar taimaka wa wajen samar da ingataccen zabe a 2023.

Ya kuma bayyana dalilin da ya sa bai kori tsohon gwamnan babban bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele duk da an alakanta shi da neman tikitin takarar shugaban kasa a APC a 2023.

  • Jihar Kaduna Za Ta Ƙarfafa Ƙawancen Tattalin Arziki Da Ƙasar Jamus
  • Sin Ta Riga Ta Bayar Da Gudunmawar Da Ake Bukata Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

A cewarsa, ba zai iya korar Emefiele daga ofis ba saboda bai fada masa burinsa ba na neman shugaban Nijeriya ba.

ADVERTISEMENT

Buhari ya bayyana hakan ne a wurin kaddamar da littafin ayyukan da ya yi tun daga 2015 zuwa 2023, wanda tsohon mai magana da yawunsa, Femi Adesina ya rubuta.

An dai kaddamar da littafin ne a hukumance a Abuja ranar Talata, Buhari ya kare manufar sake fasalin naira da Emefiele ya aiwatar, inda ya tabbatar da cewa ta taimaka wajen samar da ingantaccen zabe a 2023.

LABARAI MASU NASABA

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

Tsohon shugaban kasar ya ci gaba da cewa wadanda ke da matsala da manufar sake fasalin naira mutane ne da ke da kudade masu yawa.

Buhari ya ce, “Ba da gangan muka sauya fasanin naira ba da kuma samun karancin kudade da aka yi domin hukunta ‘yan Nijeriya ba. Dimokuradiyya tana ba mutane damar bayyana ra’ayinsu, kuma ba mu yi kokarin hana su ba. Mutane sun fahimci illar bin ra’ayinsu a zaben, kuma ba mu tilasta musu ba.

“Jihata ta Katsina an samu kyakkyawan tsari. A zaben shugaban kasa, APC ta sha kaye. Amma ta samu nasara a zaben gwamna. Watakila sun yi sakaci ne saboda suna tunanin ita ce jihata, kuma suna tunanin za su yi nasara cikin sauki. Mutane ba sa son a yi sakaci wajen gudanar da zabe domin haka zai sa a sha mamaki.

“Na sami Emefiele a ofis a lokacin da na zo a matsayin shugaban kasa, ban samu wasu kwararan hujjoji a kansa da sa in sallame shi daga matsayinsa na gwamnan CBN.

“Idan ka azabtar da mutum bisa zalunci, ba zai iya mantawa ba har tsawon rayuwarsa, don haka idan za ka hukunta mutum, dole ne ka sami kwararen hujjoji. Kuma ya kamata ka sani cewa ba za ka tabbtar a mukami ba har abada. Dole ne wata rana sai ka bar wannan mukamin da kake.

“Lokacin da aka alakanta shi da neman takaran shugaban kasa a 2023, ban tambaye shi ba, saboda bai fada wa kowa ba cewa yana da muradin zama shugaban kasa. In ba haka ba, da na cire shi tare da yi wa al’umma bayanin dalilin da ya sa.

“Babu shakka manufar sake fasalin naira ta ba mu zabuka mai matukar tsafta. Mutanen da ke da makudan kudade ne suka sami matsala da tsarin,” in ji Buhari.

Naira
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

MASU ALAKA

makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

June 26, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Next Post
Ziyarar Ministan Wajen Sin A Afirka: Zumunci Mai Dadi Ba Irin Na ’Yan Ta-more Ba

Ziyarar Ministan Wajen Sin A Afirka: Zumunci Mai Dadi Ba Irin Na ’Yan Ta-more Ba

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Ya Raba Buhunan Taki 72,000 Da Kayan Noma Kyauta Ga Manoman Zamfara

Gwamna Dauda Ya Raba Buhunan Taki 72,000 Da Kayan Noma Kyauta Ga Manoman Zamfara

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello

July 11, 2026
Gwamnati Ta Shirya Gina Gidaje 20,000 Duk Shekara Haɗin Gwuiwar  Jamus

Gwamnati Ta Shirya Gina Gidaje 20,000 Duk Shekara Haɗin Gwuiwar Jamus

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ra’ayin Al’umma Game Da Shirin Gwamnati Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 11, 2026
Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

July 11, 2026

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.