• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ake Noman Karkashi A Takaice

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Yadda Ake Noman Karkashi A Takaice
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar yadda bincike ya tabbatar, Nijeriya ce kan gaba wajen samar da Irin Karkashi, har ila yau a farkon shekarar 2018, Nijeriyar ce a kan gaba wajen fitar da Karkashin zuwa wasu kasashe na duniya.

Har wa yau, Nijeriya ce ta biyu a Afirka kuma ta bakwai a duniya wajen nomansa. Sa’annan, hada-hadar kasauwancinsa a kasuwar duniya na kara habaka, musamman a yankin Asiya da kuma Nahiyar Turai, inda kuma kasashen Japan da China suke shiga da Karkashin kasashen nasu daga Nijeriya.

  • ‘Yan Bindiga Sanye Da Hijabi Sun Farmaki Ofishin ‘Yansanda A Katsina
  • Nijeriya Na Fatan Samun Karin Masu Zuba Jari A Taron Kasuwanci Na Duniya

Bugu da kari, Kasashen Turkiyya, Indiya, Poland da kuma Netherlands, su ne a kan gaba wajen fitar da wannan Karkashi.

Wane Lokaci Ne Ya Fi Da Cewa A Shuka Karkashi:

Bincike ya nuna cewa, a yankin Kharif da ke Arewacin Kasar Indiya da kuma Kudancin Kasar, an fi yin noman Karkashi a lokacin rani, haka nan a nan Nijeriya an fi yin nomansa a wannan lokaci na rani.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Tsawon Lokacin Da Karkashi Ke Dauka Kafin Ya Girma:

Karkashi na kai wa tsawon kwana 100 zuwa 135 kafin ya gama girma baki-daya.

Ribar Nawa Ake Samu Daga Ganyensa Da Aka Sayar?

Ana iya samun akalla ribar Naira 60,036,06 a duk kadada daya da aka noma, sannan bayan an girbe shi za kuma a iya samun kudaden shiga akalla Naira 184,701,98, a kowace kadada daya, inda za a iya tara ribar da ta kimanin Naira 124,665,92.

Girbin Karkashi A Duk Kadada Guda Na Kaiwa Nawa?

Jumullar abin da ake samu bayan an yi girbi a kowace kadada na da yawan gaske, amma kuma ya danganta da ingantaccen Irin da aka yi amfani da shi wajen shuka.

Domin kuwa, zai iya yiwuwa a kowace kadada daya a samu daga kilo 200 zuwa 500.

Wane Takin Zamani Ya Fi Dacewa A Yi Amfani Da Shi?

An fi so a yi amfani da nau’in takin zamani na NPK, sannan an bayar da shawarar sanya takin NPK din buhu uku da kuma nau’in takin zamani na Urea.

A Ina Aka Fi Yin Noman Karkashi A Nijeriya?

An fi yin noman Karkashi a garuruwan Keffi, Lafiya, Doma da ke a Jihar  Nassarawa, sai kuma a Jihohin Taraba da Makurdi da ke Biniwe.

Har ila yau, ana yin remon Irin Karkashi a jihohi kamar su Ebonyi da Delta da Jigawa da Bauchi da Nassarawa da Benuwe da Maiduguri da Katsina da Taraba da sauransu.

Wane Lokaci Ya Fi Dacewa A Shuka Karkashi?

Wannan ya danganta da irin yanayin da ake ciki na lokacin yin noman, amma ya fi kyau a lokacin da ma’aunin yanayi ya kai kimanin 70.

Matakan Fara Yin Nomansa:

Zabar Gonar Da Za A Shuka Shi: Ana son a zabo kasar noman da ta fi dacewa da shuka shi, sai dai wannan abu ne mai sauki a Nijeriya; domin kuwa tana da kasar noma mai kyan gaske da za a iya shuka shi ba tare da fuskantar wata matsala ba.

Zabo Ingantaccen Iri:

Ana bukatar a samu ingantaccen Iri wanda ya kamata a shuka, inda ake da nau’ikan Irin har kala biyu, mai ruwan kasa da kuma fari.

Gyaran Gonar Da Za A Shuka Shi:

Yana da kyau kafin a fara shuka shi a tabbatar da an gyara gonar, musamman wajen cire ciyawa ta yadda zai girma da wuri kuma cikin sauri.

Ana shuka Irinsa a kasar noman da aka yi wa haro, inda ake bukatar a shuka Irin daga kilogiram 4 zuwa 5, sannan kuma ya kamata a sani cewa; a duk Irin Karkashi a kadada daya, ana samun kimanin tan 1 zuwa 1.5 a duk shekara.

Lokacin Girbe Shi:

A nan ko shakka babu, ya na kai wa akalla wata biyar kafin ya gama girma baki-daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Za Ku Inganta Rayuwarku A 2024 A Kimiyyance

Next Post

Hadin Abincin Kajin Gidan Gona Masu Saurin Girma

Related

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

4 days ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

4 days ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

2 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

2 weeks ago
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

2 weeks ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

3 weeks ago
Next Post
Hadin Abincin Kajin Gidan Gona Masu Saurin Girma

Hadin Abincin Kajin Gidan Gona Masu Saurin Girma

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

August 27, 2025
Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.