ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ake Noman Karkashi A Takaice

by Abubakar Abba
3 years ago
Karkashi

Kamar yadda bincike ya tabbatar, Nijeriya ce kan gaba wajen samar da Irin Karkashi, har ila yau a farkon shekarar 2018, Nijeriyar ce a kan gaba wajen fitar da Karkashin zuwa wasu kasashe na duniya.

Har wa yau, Nijeriya ce ta biyu a Afirka kuma ta bakwai a duniya wajen nomansa. Sa’annan, hada-hadar kasauwancinsa a kasuwar duniya na kara habaka, musamman a yankin Asiya da kuma Nahiyar Turai, inda kuma kasashen Japan da China suke shiga da Karkashin kasashen nasu daga Nijeriya.

  • ‘Yan Bindiga Sanye Da Hijabi Sun Farmaki Ofishin ‘Yansanda A Katsina
  • Nijeriya Na Fatan Samun Karin Masu Zuba Jari A Taron Kasuwanci Na Duniya

Bugu da kari, Kasashen Turkiyya, Indiya, Poland da kuma Netherlands, su ne a kan gaba wajen fitar da wannan Karkashi.

ADVERTISEMENT

Wane Lokaci Ne Ya Fi Da Cewa A Shuka Karkashi:

Bincike ya nuna cewa, a yankin Kharif da ke Arewacin Kasar Indiya da kuma Kudancin Kasar, an fi yin noman Karkashi a lokacin rani, haka nan a nan Nijeriya an fi yin nomansa a wannan lokaci na rani.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Tsawon Lokacin Da Karkashi Ke Dauka Kafin Ya Girma:

Karkashi na kai wa tsawon kwana 100 zuwa 135 kafin ya gama girma baki-daya.

Ribar Nawa Ake Samu Daga Ganyensa Da Aka Sayar?

Ana iya samun akalla ribar Naira 60,036,06 a duk kadada daya da aka noma, sannan bayan an girbe shi za kuma a iya samun kudaden shiga akalla Naira 184,701,98, a kowace kadada daya, inda za a iya tara ribar da ta kimanin Naira 124,665,92.

Girbin Karkashi A Duk Kadada Guda Na Kaiwa Nawa?

Jumullar abin da ake samu bayan an yi girbi a kowace kadada na da yawan gaske, amma kuma ya danganta da ingantaccen Irin da aka yi amfani da shi wajen shuka.

Domin kuwa, zai iya yiwuwa a kowace kadada daya a samu daga kilo 200 zuwa 500.

Wane Takin Zamani Ya Fi Dacewa A Yi Amfani Da Shi?

An fi so a yi amfani da nau’in takin zamani na NPK, sannan an bayar da shawarar sanya takin NPK din buhu uku da kuma nau’in takin zamani na Urea.

A Ina Aka Fi Yin Noman Karkashi A Nijeriya?

An fi yin noman Karkashi a garuruwan Keffi, Lafiya, Doma da ke a Jihar  Nassarawa, sai kuma a Jihohin Taraba da Makurdi da ke Biniwe.

Har ila yau, ana yin remon Irin Karkashi a jihohi kamar su Ebonyi da Delta da Jigawa da Bauchi da Nassarawa da Benuwe da Maiduguri da Katsina da Taraba da sauransu.

Wane Lokaci Ya Fi Dacewa A Shuka Karkashi?

Wannan ya danganta da irin yanayin da ake ciki na lokacin yin noman, amma ya fi kyau a lokacin da ma’aunin yanayi ya kai kimanin 70.

Matakan Fara Yin Nomansa:

Zabar Gonar Da Za A Shuka Shi: Ana son a zabo kasar noman da ta fi dacewa da shuka shi, sai dai wannan abu ne mai sauki a Nijeriya; domin kuwa tana da kasar noma mai kyan gaske da za a iya shuka shi ba tare da fuskantar wata matsala ba.

Zabo Ingantaccen Iri:

Ana bukatar a samu ingantaccen Iri wanda ya kamata a shuka, inda ake da nau’ikan Irin har kala biyu, mai ruwan kasa da kuma fari.

Gyaran Gonar Da Za A Shuka Shi:

Yana da kyau kafin a fara shuka shi a tabbatar da an gyara gonar, musamman wajen cire ciyawa ta yadda zai girma da wuri kuma cikin sauri.

Ana shuka Irinsa a kasar noman da aka yi wa haro, inda ake bukatar a shuka Irin daga kilogiram 4 zuwa 5, sannan kuma ya kamata a sani cewa; a duk Irin Karkashi a kadada daya, ana samun kimanin tan 1 zuwa 1.5 a duk shekara.

Lokacin Girbe Shi:

A nan ko shakka babu, ya na kai wa akalla wata biyar kafin ya gama girma baki-daya.

Karkashi
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Hadin Abincin Kajin Gidan Gona Masu Saurin Girma

Hadin Abincin Kajin Gidan Gona Masu Saurin Girma

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

September 11, 2026
Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

September 11, 2026
Sanata yari

Gwarzon Ɗan Siyasa Na Shekarar 2026 Sanata Abdul’Aziz Abubakar Yari

September 11, 2026
Kasar Sin Za Ta Taimaka Wajen Bunkasa Wadatar Makamashi Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Za Ta Taimaka Wajen Bunkasa Wadatar Makamashi Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 11, 2026
SAW

Ɗabi’un Annabi (SAW) Kan Abubuwa Na Al’adar Rayuwa

September 11, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Horar Da Malamai 250,000

Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Horar Da Malamai 250,000

September 11, 2026
Karkashi

Sojoji Sun Ceto Mutane 13 Da ’Yan Bindiga Suka Yi Garkuwa Da Su

September 11, 2026
Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

September 11, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang

September 11, 2026
Karkashi

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.