ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ake Noman Karkashi A Takaice

by Abubakar Abba
2 years ago
Karkashi

Kamar yadda bincike ya tabbatar, Nijeriya ce kan gaba wajen samar da Irin Karkashi, har ila yau a farkon shekarar 2018, Nijeriyar ce a kan gaba wajen fitar da Karkashin zuwa wasu kasashe na duniya.

Har wa yau, Nijeriya ce ta biyu a Afirka kuma ta bakwai a duniya wajen nomansa. Sa’annan, hada-hadar kasauwancinsa a kasuwar duniya na kara habaka, musamman a yankin Asiya da kuma Nahiyar Turai, inda kuma kasashen Japan da China suke shiga da Karkashin kasashen nasu daga Nijeriya.

  • ‘Yan Bindiga Sanye Da Hijabi Sun Farmaki Ofishin ‘Yansanda A Katsina
  • Nijeriya Na Fatan Samun Karin Masu Zuba Jari A Taron Kasuwanci Na Duniya

Bugu da kari, Kasashen Turkiyya, Indiya, Poland da kuma Netherlands, su ne a kan gaba wajen fitar da wannan Karkashi.

ADVERTISEMENT

Wane Lokaci Ne Ya Fi Da Cewa A Shuka Karkashi:

Bincike ya nuna cewa, a yankin Kharif da ke Arewacin Kasar Indiya da kuma Kudancin Kasar, an fi yin noman Karkashi a lokacin rani, haka nan a nan Nijeriya an fi yin nomansa a wannan lokaci na rani.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Tsawon Lokacin Da Karkashi Ke Dauka Kafin Ya Girma:

Karkashi na kai wa tsawon kwana 100 zuwa 135 kafin ya gama girma baki-daya.

Ribar Nawa Ake Samu Daga Ganyensa Da Aka Sayar?

Ana iya samun akalla ribar Naira 60,036,06 a duk kadada daya da aka noma, sannan bayan an girbe shi za kuma a iya samun kudaden shiga akalla Naira 184,701,98, a kowace kadada daya, inda za a iya tara ribar da ta kimanin Naira 124,665,92.

Girbin Karkashi A Duk Kadada Guda Na Kaiwa Nawa?

Jumullar abin da ake samu bayan an yi girbi a kowace kadada na da yawan gaske, amma kuma ya danganta da ingantaccen Irin da aka yi amfani da shi wajen shuka.

Domin kuwa, zai iya yiwuwa a kowace kadada daya a samu daga kilo 200 zuwa 500.

Wane Takin Zamani Ya Fi Dacewa A Yi Amfani Da Shi?

An fi so a yi amfani da nau’in takin zamani na NPK, sannan an bayar da shawarar sanya takin NPK din buhu uku da kuma nau’in takin zamani na Urea.

A Ina Aka Fi Yin Noman Karkashi A Nijeriya?

An fi yin noman Karkashi a garuruwan Keffi, Lafiya, Doma da ke a Jihar  Nassarawa, sai kuma a Jihohin Taraba da Makurdi da ke Biniwe.

Har ila yau, ana yin remon Irin Karkashi a jihohi kamar su Ebonyi da Delta da Jigawa da Bauchi da Nassarawa da Benuwe da Maiduguri da Katsina da Taraba da sauransu.

Wane Lokaci Ya Fi Dacewa A Shuka Karkashi?

Wannan ya danganta da irin yanayin da ake ciki na lokacin yin noman, amma ya fi kyau a lokacin da ma’aunin yanayi ya kai kimanin 70.

Matakan Fara Yin Nomansa:

Zabar Gonar Da Za A Shuka Shi: Ana son a zabo kasar noman da ta fi dacewa da shuka shi, sai dai wannan abu ne mai sauki a Nijeriya; domin kuwa tana da kasar noma mai kyan gaske da za a iya shuka shi ba tare da fuskantar wata matsala ba.

Zabo Ingantaccen Iri:

Ana bukatar a samu ingantaccen Iri wanda ya kamata a shuka, inda ake da nau’ikan Irin har kala biyu, mai ruwan kasa da kuma fari.

Gyaran Gonar Da Za A Shuka Shi:

Yana da kyau kafin a fara shuka shi a tabbatar da an gyara gonar, musamman wajen cire ciyawa ta yadda zai girma da wuri kuma cikin sauri.

Ana shuka Irinsa a kasar noman da aka yi wa haro, inda ake bukatar a shuka Irin daga kilogiram 4 zuwa 5, sannan kuma ya kamata a sani cewa; a duk Irin Karkashi a kadada daya, ana samun kimanin tan 1 zuwa 1.5 a duk shekara.

Lokacin Girbe Shi:

A nan ko shakka babu, ya na kai wa akalla wata biyar kafin ya gama girma baki-daya.

Karkashi
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Hadin Abincin Kajin Gidan Gona Masu Saurin Girma

Hadin Abincin Kajin Gidan Gona Masu Saurin Girma

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.