• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Ceto Sauran Mutanen Da Aka Yi Garkuwa Da Su Daga Ukuba, In Ji Iyalan Al-Kadiriyah

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
A Ceto Sauran Mutanen Da Aka Yi Garkuwa Da Su Daga Ukuba, In Ji Iyalan Al-Kadiriyah
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

Iyalan Al-Kadiriyah na yankin Okekere da ke Ilorin, Jihar Kwara, sun yi kira da a hada karfi da karfe domin ganin an sako wadanda aka yi garkuwa da su a fadin kasar nan.

Iyalan a yayin da suke murnar sakin ‘ya’yansu mata da masu garkuwa da su suka yi, sun bukaci shugabanin Nijeriya da ‘yan kasar da kada su yi watsi da wadanda har yanzu ake garkuwa da su.

  • Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya
  • Kofin Afirka 2023: Yadda Manyan Kasashe Ke Tafka Abin Kunya

Biyar daga cikin ’yan uwa mata na ahalin Al-Kadriyar shida da aka yi garkuwa da su a Bwari da ke Abuja a farkon watan Janairu, sun samu ‘yanci.

Haka kuma, wani da aka yi garkuwa da shi, Suleiman Sabo, an kubutar da shi daga hannun masu garkuwa da mutane a Sauka, daura da titin filin jirgin sama, Abuja.

Jami’an rundunar ‘yansanda da ke yaki da masu garkuwa da mutane a Babban Birnin Tarayya, a kokarin hadin gwiwa tare da sojojin Nijeriya, sun ceto mutanen da aka yi garkuwa da su a yankin Zuma 1 da ke Karamar Hukumar Bwari, wadanda aka yi garkuwa da su a ranar 2 ga Janairun 2024.

Da take tabbatar da rahoton, kakakin rundunar ‘yansandan Babban Birnin Tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, ta ce ‘yansandan sun yi nasarar ceto wadanda lamarin ya rutsa da su a dajin Kajuru a Jihar Kaduna da misalin karfe 11:30 na dare.

A cikin wata sanarwa da suka fitar, ta hannun daya cikin ahalin Al-Kadiriyah Sherifdeen, sun ce: “A wannan lokacin na murna, kar mu manta da wadanda har yanzu suke fuskantar wahalhalu a hannun ‘yan bindiga, mu ci gaba da yi musu addu’ar Allah ya dawo da su lafiya. Ya zama wajibi mu a matsayinmu na al’umma mu tallafa wa juna da kuma daukaka juna a lokutan da suke shan wahala.”

Sherifdeen ya yi kira da a yi addu’o’in samun lafiya ga rayukan wadanda suka mutu a hannu masu garkuwa da mutane.

Ya kuma mika godiyarsa ga jami’an tsaro, hukumomi, da duk wadanda suka jajirce wajen ganin an ceto ‘ya’ya matan.

Har ila yau, shugaban kungiyar ‘yan asalin Ilorin Masarautar IEDPU na kasa, Alhaji Abdulmumini AbdulMalik, ya sake jaddada bukatar gwamnati a dukkan matakai na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa.

Ya gode wa Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazak, Sarkin Ilorin, Alhaji Ibrahim Sulu-Gambari, Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na Zamani, Farfesa Issa Ali Patanmi da sauran al’ummar Masarautar Ilorin, musamman, don goyon baya da addu’o’in da aka bai wa iyalan Al-Kadiriyah a lokacin da aka bayyana irin manancin halin da suka tsinci kansu.”

LEADERSHIP Hausa ta bayar da rahoton cewa an sace ‘yan matan ne tare da mahaifinsu da kuma wasu mazauna unguwar, inda nan take aka sako mahaifinsu aka umarce su da ya biya kudin fansa kimanin Naira miliyan 60 ga yaran.

Daya daga cikin ‘yan uwa mata mai suna Nabeeha, daga baya masu garkuwa da mutane suka kashe ta saboda ba su biya kudin fansar da gaggawa.

A halin da ake ciki kuma, a yayin aikin ceton, an kama wani da ake zargi mai suna Muhammad Abel, mai shekaru 32, daga Jihar Kogi, tare da kwato bindigar LAR guda daya da harsashi guda goma 10.

A jiya kuma aka samu rahoton an sako wasu mutum bakwai da aka yi garkuwa da su a rukunin gidajen Sagwari da ke Karamar Hukumar Bwari a Babban Birnin Tarayya Abuja.

An sace su ne kwanaki da suka wuce lokacin da ‘yan bindiga suka kai farmaki a gidan da misalin karfe 8 na dare

Wata daga cikin wadanda abin ya shafa, Talatu Salihu, daliba mai matakin digiri na 500 akan Laburare da Kimiyyar Yada Labarai, Jami’ar Bayero Kano (BUK)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Rantsar Da Ododo A Matsayin Gwamnan Kogi

Next Post

Jariri Ya Yi Batan Dabo A Asibitin Waziri Gidado Da Ke Kano

Related

‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

4 weeks ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

4 weeks ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

3 months ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

4 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

4 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

4 months ago
Next Post
Jariri Ya Yi Batan Dabo A Asibitin Waziri Gidado Da Ke Kano

Jariri Ya Yi Batan Dabo A Asibitin Waziri Gidado Da Ke Kano

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.