ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Ceto Sauran Mutanen Da Aka Yi Garkuwa Da Su Daga Ukuba, In Ji Iyalan Al-Kadiriyah

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Ceto

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

Iyalan Al-Kadiriyah na yankin Okekere da ke Ilorin, Jihar Kwara, sun yi kira da a hada karfi da karfe domin ganin an sako wadanda aka yi garkuwa da su a fadin kasar nan.

Iyalan a yayin da suke murnar sakin ‘ya’yansu mata da masu garkuwa da su suka yi, sun bukaci shugabanin Nijeriya da ‘yan kasar da kada su yi watsi da wadanda har yanzu ake garkuwa da su.

  • Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya
  • Kofin Afirka 2023: Yadda Manyan Kasashe Ke Tafka Abin Kunya

Biyar daga cikin ’yan uwa mata na ahalin Al-Kadriyar shida da aka yi garkuwa da su a Bwari da ke Abuja a farkon watan Janairu, sun samu ‘yanci.

Haka kuma, wani da aka yi garkuwa da shi, Suleiman Sabo, an kubutar da shi daga hannun masu garkuwa da mutane a Sauka, daura da titin filin jirgin sama, Abuja.

Jami’an rundunar ‘yansanda da ke yaki da masu garkuwa da mutane a Babban Birnin Tarayya, a kokarin hadin gwiwa tare da sojojin Nijeriya, sun ceto mutanen da aka yi garkuwa da su a yankin Zuma 1 da ke Karamar Hukumar Bwari, wadanda aka yi garkuwa da su a ranar 2 ga Janairun 2024.

Da take tabbatar da rahoton, kakakin rundunar ‘yansandan Babban Birnin Tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, ta ce ‘yansandan sun yi nasarar ceto wadanda lamarin ya rutsa da su a dajin Kajuru a Jihar Kaduna da misalin karfe 11:30 na dare.

A cikin wata sanarwa da suka fitar, ta hannun daya cikin ahalin Al-Kadiriyah Sherifdeen, sun ce: “A wannan lokacin na murna, kar mu manta da wadanda har yanzu suke fuskantar wahalhalu a hannun ‘yan bindiga, mu ci gaba da yi musu addu’ar Allah ya dawo da su lafiya. Ya zama wajibi mu a matsayinmu na al’umma mu tallafa wa juna da kuma daukaka juna a lokutan da suke shan wahala.”

Sherifdeen ya yi kira da a yi addu’o’in samun lafiya ga rayukan wadanda suka mutu a hannu masu garkuwa da mutane.

Ya kuma mika godiyarsa ga jami’an tsaro, hukumomi, da duk wadanda suka jajirce wajen ganin an ceto ‘ya’ya matan.

Har ila yau, shugaban kungiyar ‘yan asalin Ilorin Masarautar IEDPU na kasa, Alhaji Abdulmumini AbdulMalik, ya sake jaddada bukatar gwamnati a dukkan matakai na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa.

Ya gode wa Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazak, Sarkin Ilorin, Alhaji Ibrahim Sulu-Gambari, Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na Zamani, Farfesa Issa Ali Patanmi da sauran al’ummar Masarautar Ilorin, musamman, don goyon baya da addu’o’in da aka bai wa iyalan Al-Kadiriyah a lokacin da aka bayyana irin manancin halin da suka tsinci kansu.”

LEADERSHIP Hausa ta bayar da rahoton cewa an sace ‘yan matan ne tare da mahaifinsu da kuma wasu mazauna unguwar, inda nan take aka sako mahaifinsu aka umarce su da ya biya kudin fansa kimanin Naira miliyan 60 ga yaran.

Daya daga cikin ‘yan uwa mata mai suna Nabeeha, daga baya masu garkuwa da mutane suka kashe ta saboda ba su biya kudin fansar da gaggawa.

A halin da ake ciki kuma, a yayin aikin ceton, an kama wani da ake zargi mai suna Muhammad Abel, mai shekaru 32, daga Jihar Kogi, tare da kwato bindigar LAR guda daya da harsashi guda goma 10.

A jiya kuma aka samu rahoton an sako wasu mutum bakwai da aka yi garkuwa da su a rukunin gidajen Sagwari da ke Karamar Hukumar Bwari a Babban Birnin Tarayya Abuja.

An sace su ne kwanaki da suka wuce lokacin da ‘yan bindiga suka kai farmaki a gidan da misalin karfe 8 na dare

Wata daga cikin wadanda abin ya shafa, Talatu Salihu, daliba mai matakin digiri na 500 akan Laburare da Kimiyyar Yada Labarai, Jami’ar Bayero Kano (BUK)

Ceto
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

April 25, 2026
An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

April 25, 2026
Next Post
Jariri Ya Yi Batan Dabo A Asibitin Waziri Gidado Da Ke Kano

Jariri Ya Yi Batan Dabo A Asibitin Waziri Gidado Da Ke Kano

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.