• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Idan Na Kalli ‘Certificates’ Da Na Samu Silar Rubutu Ina Jin Dadi Sosai – Fatima

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Fatima

A karkashen tattaunawar da marubuciya FATIMA SUNUSI RABI’U ta yi da shafin ADABI, ta bayyana irin nasarorin da ta samu a fannin rubutu, haka nan da kalubalen da abin ya kunsa kamar yadda PRINCESS FATIMA ZARAH MAZADU ta aiko mana kamar haka:

Wanne irin nasarori ki ka samu game da rubutu?

Alhamdu lillah na samu nasarori sosai a silar rubutu, sanin ma mutane nasara ce. Domin silar rubutu na san mutane da dama a jahohi mabanbanta har ma da kasashen ketare ana zumunci da zama na amana. Haka a 2021 na samu nasarar zuwa gwarzuwa ta daya a gasar Tambari Writers an karrama ni kuma an ba ni na kashewa. Haka na samu nasarar zuwa gwarzuwa ta biyu a wata gasa ta Wiwan ita ma an karrama ni. A wannan shekarar kuma ta 2023 labarina ya zamo daya a cikin 13 a gasar Gusau Institute an ba ni Certificate, sannan akwai kananun alkhairai sosai da na cimma nasara duk a silar rubutu.

 

Me za ki ce da masu karanta littattafanki?

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

Tsakani na da masu karatu sai sam-barka akwai amana sosai, sai dai na yi musu fatan alkhairi. Kalubale bai wuce na wasu da kake dangantaka da su ba ka ji ana ce maka, baka da aikin yi, rubutu ai wahalar da kai ne, koma a yi maka kallon kamar ba ka san me kake ba. Sauran kalubale kam ba na kallonsu da yazo idan ya wuce nake manta komi.

 

Mene ne burinki na gaba game da rubutu?

Kowa yana da buri a rayuwarsa wasu su cika wasu kuma har ka rasu da burinka, ina fatan Allah ya cika mini burikana na alkhairi, wasu daga ciki, ina fatan na yi rubutun da zai zaga ko ina a duniya na shiga cikin wadanda za a dinga kwatance da su kuma yin alfahari da rubutunsu. Sannan ina da burin ganin na bude wata gidauniya domin taimakon marayu da mabukata.

 

Wanne irin yabo ki ke samu wajen masu karanta labaranki?

Yabawa ta nawa kuwa, gaskiya ina samun mutane da ke yabawa wasu har kira a waya a yaba maka. Bata rai bai wuce na idan kana littafin kudi ba ka dan sami wani akasin da baka yi rubutu ba ka ji ana ta magana musamman ta ‘pribate’ cewa ka amshi kudi amma shuru babu ‘posting’. Wani lokacin dole ne take sa a ji ka shuru kwana biyu, amma kuma da zarar ka ci gaba sai komi ya wuce.

 

Wanne abu ne idan ki ka tuna shi yake saka ki farin ciki?

Idan na kalli ‘Certificates’ dina wadanda silar rubutu na same su, ina jin dadi sosai.

 

Bayan rubutu kina sana’a?

Eh! ina sana’a kam, ko ince sana’o’i ma. AlhamduLillah.

 

Ya ki ke iya hada sana’arki da kuma rubutu?

[Dariya] komai da lokacinsa, sannan gaskiya ni yanzu na tsara yadda nake rubutuna ba kamar baya ba, muna da kungiya ta gwawurtattu uku to mun tsara a duk shekara zamu fitar da labarai guda biyu ne, don haka komai yana da lokacinsa.

 

Kamar wanne lokaci ki ka fi jin dadin yin rubutu?

To idan har ina da lokaci kuma ina jin yin rubutun to ina iya yi, kawai dai na fi son yanayin da zan tsince ni shuru babu hayaniya, ina yawan yin rubutu bayan sallar isha’i, dana yi sai na kwanta na yi bacci.

 

Me za ki ce da masu karanta littafinki?

Ina kaunarsu a kowanne lokaci, kuma ina musu fatan alkhairi sannan ina fatan su ci gaba da bina a duk lokacin da na saki sabon littafi. Ina kaunarsu kamar yadda suke kaunata da littattafaina.

 

Ko kina da wadanda za ki gaisar?

To ma sha Allahu, ina gaida kanwata Dr Maryamah Ibrahim marubuciya da aminyata Rukayya Ibrahim Lawal sai gawurtattu uku Badi’at Mrs Bukhari da Ummu Maheer Miss Green sannan ina gaishe da Auntyna Hadiza Ibrahim D Auta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)
Adabi

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

September 26, 2025
Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili
Adabi

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

April 19, 2025
Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa
Al'adu

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

December 30, 2024
Next Post
Li Qiang Ya Tattauna Da Kwararrun ‘Yan Kasashen Waje Dake Kasar Sin

Li Qiang Ya Tattauna Da Kwararrun ‘Yan Kasashen Waje Dake Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
Abduljabbar

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

October 17, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Kasar Sin: Sin Za Ta Kyautata Matakan Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Kasar Sin: Sin Za Ta Kyautata Matakan Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.