• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kiristoci Kada Su Damu Da Takarar Musulmi 2 – Shugaban Jam’iyyar APC

by Sadiq
3 years ago
APC

Shugaban jam’iyyar APC, mai mulkin Nijeriya, Sanata Abdullahi Adamu, ya shawarci mabiya addinin Kirista da su daina wata fargaba a kan tsayar da dantakarar shugaban kasa na 2023, Musulmi da mataimakinsa Musulmi da jam’iyyar ta yi.

Shugaban ya ce yanayin halin da siyasar kasar ke ciki ne a yanzu ya janyo hakan, wanda idan har jam’iyyar na son ta ci zaben 2023 sai ta yi hakan, amma ba abu ne da wani zai so ba a ce an yi wannan tsari.

  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Umarnin Sayar Da Takin Noma Miliyan 1.7 Ga Manoman Jihar
  • Ya Kamata Buhari Ya Gaggauta Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU – Femi Falana

Sanata Adamu ya ce zaben Kashim Shettima a matsayin mataimakin Bola Ahmed Tinubu, abu ne yin Allah.

Da yake yi wa manema labarai bayani bayan wata ganawar sirri da shugaban kasa Muhammadu Buhari, a Daura, Jihar Katsina a jiya Laraba, tsohon gwamnan na Nasarawa, ya ce bai kamata wannan zabi ya zama abin korafi ba ga mabiya addinin Kirista.

“Gaskiyar lamari shi ne, ba abin da Allah yake yi haka kawai. Allah yana da dalilinsa na samar da manyan addinai biyu a kasar nan, kuma kowane daga cikinsu, yana da mutanen da suke da dalilin binsa kuma suna da hakki suma.”

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

”Akwai lokacin da Kirista ya jagoranci kasar nan. Yanzu kuma lokaci ne da Musulmi ke shugabantar kasar, ba za mu musanta wanna ba. Ba za mu iya samun lalle abin da muke so ba a wani lokaci, a ce dukkanin mu, mun amince da abu daya,” in ji shi.

Ya kuma kara da bayanin cewa, ” Ba lalle ba ne sai dukkaninmu mun kasance Musulmi ba ko kiristoci. Nufi ne na Allah a wannan lokacin cewa Shettima zai kasance mataimakin shugaban wannan babbar kasa, idan muka ci zabe. Abin da muke fata da kuma addu’a, wanda kuma muna kokarin cin zaben.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
Siyasa

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
Dangantaka Tsakanin Nijeriya da Sin Ta Kara Karfi Yayin Da Jirgi Ya Fara Tashi Zuwa Guangzhou

Dangantaka Tsakanin Nijeriya da Sin Ta Kara Karfi Yayin Da Jirgi Ya Fara Tashi Zuwa Guangzhou

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.