ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Mutanen Buhari Suka Sha Kaye A Zaben Fitar Da Gwanin APC A Kano

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Buhari

Tsofaffin mataimaka na musamman ga Shugaban Kasa Muhammadu Buhari wadanda suka tsaya takara a jam’iyyar APC na neman kujerar gwamna da majalisar dattawa da na majalisar wakilai a Jihar Kano dukkan su sun sha kaye a zaben fitar da gwani.

Sun dai hada da Sha’aban Sharada, wanda shi ne tsohon mataimaki na musam-man ga shugaban kasa kan watsa labarai, wanda a halin yanzu haka shi ne shuga-ban kwamitin majalisar wakilai kan fasahar tsaron kasa da tsohon mataimaki na musamman kan kafafen yada labarai na zamani, Bashir Ahmad da kuma tsohon mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan bunkasa zamantakewa, Ismaeel Ahmed duk sun sha kaye a zaben fitar da gwani da ya gabata a Jihar Kano.

  • Kamfanonin Kasar Sin Sun Ba Da Kyauta Ga Daliban Ghana Da Ke Fama Da Talauci

Sun dai sha kayen ne a hannun ‘yan takarar da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya mara wa baya.

ADVERTISEMENT

Shi dai Sha’aban ya tsaya takarar gwamna ne a karkashin jam’iyyar, yayin da Bashir ya nemi samun tikitin takarar dan majalisa na mazanar Albasu/Gaya/Ajingi, sai kuma Ismaeel da ya nemi tikitin takarar dan majalisar dattawa na Kano ta tsakiya.

Ismaeel ya bayyana janyewar takararsa mintina kadan kafin gudanar da zaben fitar da gwani. Amma shi Sha’aban da kuma Bashir an gudanar da zaben fitar da gwanin da su wadanda suka sha kaye.
Bayanai dai sun nuna cewa, Ismaeel ya janye takararsa ne bayan da gwamna ya tabbatar masa da cewa Abdulsalam Abdulkarim Zaura zai bai wa tikitin takara.

LABARAI MASU NASABA

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

Sha’aban dai ya samu kuri’u 30, yayin da abokin karawarsa mataimakin gwamna, Nasiru Yusuf Gawuna wanda ya lashe zaben ya samu kuri’u 2,289.

Bashir dai ya samu kuri’a 16, yayin da abokin karawarsa da ya lashe zaben, Abdul-lahi Mahmoud Gaya ya samu kuri’u 109.

Masu sharhi kan zaben Kano sun bayyana cewa sakamakon zaben fitar da gwani na takarar gwamnan bai zo da mamaki ba, saboda Sha’aban yana takun-saka da gwamna da kuma shugabannin jam’iyyar APC na jihar tun a shekarar 2021.

Shi kuma Bashir a tunaninsa zai iya samun tikitin takarar dan majalisar wakilai ci-kin ruwan sanyi tun da dai ya kasance yaro ne ga fadar shugaban kasa kamar dai abokinsa Sha’aban, amma bai yi nasara ba.

Majiyar ta tabbatar da cewa, lokacin da Bashir ya bayyana wa shugaban kasa a niyarsa ta tsayawa takara ya amince da bukatarsa kamar dai sauran ‘yan takara da suka bayyana masa aniyarsu. Amma kuma hakan bai hana shi shan kaye ba.

Shi dai Bashir ya zargi shugabannin jam’iyyar a jihar da yin masa magudi a zaben, inda ya yi zargin an yi amfani da ‘yan daba a kansa da kuma magoya bayansa wajen tursasa musu barin wurin zaben.

Masu saka ido a zaben sun bayyana cewa bayan rashin gogewa a siyasar mazaba, babban abin da ya sa mutanen Buhari suka sha kaye shi ne, shugaban kasa bai nuna sha’awa a cikin takararsu ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

December 19, 2025
‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

December 19, 2025
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027
Tambarin Dimokuradiyya

NNPP Ta Buƙaci INEC Ta Yi Watsi Da Tarukan Jam’iyyar Da Kwankwaso Zai Jagoranta

November 28, 2025
Next Post
Jam’iyyar ZLP Ta Tsayar Da Dan Takarar Gwamna A Jihar Kano

Jam'iyyar ZLP Ta Tsayar Da Dan Takarar Gwamna A Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.