• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Tsugune Ba Ta Kare Ba Kan Zargin Aringizon Kasafin 2024 -PDP

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Har Yanzu Tsugune Ba Ta Kare Ba Kan Zargin Aringizon Kasafin 2024 -PDP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PDP ta nunar da cewa har yanzu fa tsugune ba ta kare ba dangane da zargin aringizon kasafin kudin 2024 da Sanata Abduk Ningi ya kwarmata. Inda ta yi kira ga Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sake yin nazari da kuma gudanar da kwakkwaran bincike na gaggawa dangane da kasafin kudin.

Sakataren yada labarai na jam’iyyar na kasa, Debo Ologunagba, ya fitar, da wata sanarwa da ta bayyana cewa PDP tana nan kan bakanta na ganin shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio ya gurfana a hukumar yaki da cin hanci da rashawa domin a bincike shi kan yadda naira biliyan 108 na Jihar Akwa Ibom suka bace da kuma naira biliyan 86 da aka bayar da kwangila ba bisa ka’ida ba a lokacin yana gwamna da kuma ministan kula da bunkasa yankin Neja Delta.

  • Ɗiawara Ya Fice Daga Tawagar Faransa Bayan An Hana ‘Yan Wasa Yin Azumi
  • An Fara Taron Kasa Da Kasa Kan Tsarin Dimokuradiyya Karo Na Uku A Nan Birnin Beijing

Haka kuma jam’iyyar ta caccaki Sanata Akpabio da shugabannin APC kan kawar da hankalin mutane na rashin gudanar da bincike a fili na zaargin cusa naira tiriliyan 3.7 da aka yi a cikin kasafin kudin 2024.

“Jam’iyyar PDP ta tabbatar da cewa idan aka tsana bincike za a gano asalin gaskiya game da arangizo a kasafin kudin 2024 da kuma adadin yawan kudaden da aka raba wa ‘yan majalisa na APC,” in ji sanarwar.

Ta kara da cewa wannan lamarin da ya faru ya tabbatar da cewa akwai masu hana ruwa gudu a cikin APC wajen gudanar da shugabancin Akpabio a zauren majalisa wadannda ba su damu da halin da talakawan Nijeriya ke ciki ba.

Labarai Masu Nasaba

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

 “Abin bakin ciki ne a irin wannan yanayin da Nijeriya ke fama da matsin tattalin arziki a ce shugabannin APC a zauren majalisa suna kin bayyana gaskiya kan zargin almundahanan kan kuaden da za a kawo wa ‘yan Nijeriya sauki a rayuwarsu.”

PDP ta ce Akpabio da ke shugabantar APC a zauren majalisa babu wata barazana ko dakatarwa da zai hana ‘yan adawa fallasa arangizon kudaden al’umma ta hanyar fitar da  sanarwa, rubuce-rubuce a kafaken yada labarai wajen ganin an gudanar da bincike kan zargin yin cushe a kasafin kudi.

Sanarwar ta bayyana cewa jam’iyyar PDP da ‘yan Nijeriya ba sa shakkan shugabannin APC a zauren majalisa, domin wannan cin hanci ne karara a bayyanar jama’a, amma ake kokarin yin rufa-rufa.

Ta ce rashin gudanar da bincike kan zargin cushe a kasafin kudin zai taba kimar majalisar kasa da kuma lalata ayyukan ‘yan majalisa da tsarin mulki da dora musu na gudanar da bincike kan yadda ake kashe kudaden al’umma, sannan kuma ya taba kimar dimokuradiyyar kasar nan idan har aka kasa gudanar da binciken gaggawa.

A cewar PDP, idan har Sanata Akpabio zai yi adalci, to ya gaggauta janye dakatarwar da aka yi wa Sanata Abdul Ningi tare da barin a gudanar da bincike kan arangizon naira tiriliyan 3.7 a cikin kasafin kudin 2024.

Sanarwar ta ce, “Jam’iyyarmu tana aiki kafada da kafada da ‘yan Nijeriya kuma ba za su janye ba har sai Sanata Akpabio ya bari an gudanar da sahihin bincike kan wannan labari da ya zartar da hukunci bisa kuskure.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Aiwatar Da Haramcin Kamun Kifi Na Tsawon Shekaru 10 A Kogin Yangtze

Next Post

Kasar Sin Ta Janyo Jarin Waje Har Dala Biliyan 29.8 A Janairu Da Fabrairun Bana

Related

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

8 hours ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

9 hours ago
Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

1 week ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

1 week ago
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

1 week ago
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

4 weeks ago
Next Post
kasar sin

Kasar Sin Ta Janyo Jarin Waje Har Dala Biliyan 29.8 A Janairu Da Fabrairun Bana

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

July 11, 2025
FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.