• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Tsugune Ba Ta Kare Ba Kan Zargin Aringizon Kasafin 2024 -PDP

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Har Yanzu Tsugune Ba Ta Kare Ba Kan Zargin Aringizon Kasafin 2024 -PDP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PDP ta nunar da cewa har yanzu fa tsugune ba ta kare ba dangane da zargin aringizon kasafin kudin 2024 da Sanata Abduk Ningi ya kwarmata. Inda ta yi kira ga Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sake yin nazari da kuma gudanar da kwakkwaran bincike na gaggawa dangane da kasafin kudin.

Sakataren yada labarai na jam’iyyar na kasa, Debo Ologunagba, ya fitar, da wata sanarwa da ta bayyana cewa PDP tana nan kan bakanta na ganin shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio ya gurfana a hukumar yaki da cin hanci da rashawa domin a bincike shi kan yadda naira biliyan 108 na Jihar Akwa Ibom suka bace da kuma naira biliyan 86 da aka bayar da kwangila ba bisa ka’ida ba a lokacin yana gwamna da kuma ministan kula da bunkasa yankin Neja Delta.

  • Ɗiawara Ya Fice Daga Tawagar Faransa Bayan An Hana ‘Yan Wasa Yin Azumi
  • An Fara Taron Kasa Da Kasa Kan Tsarin Dimokuradiyya Karo Na Uku A Nan Birnin Beijing

Haka kuma jam’iyyar ta caccaki Sanata Akpabio da shugabannin APC kan kawar da hankalin mutane na rashin gudanar da bincike a fili na zaargin cusa naira tiriliyan 3.7 da aka yi a cikin kasafin kudin 2024.

“Jam’iyyar PDP ta tabbatar da cewa idan aka tsana bincike za a gano asalin gaskiya game da arangizo a kasafin kudin 2024 da kuma adadin yawan kudaden da aka raba wa ‘yan majalisa na APC,” in ji sanarwar.

Ta kara da cewa wannan lamarin da ya faru ya tabbatar da cewa akwai masu hana ruwa gudu a cikin APC wajen gudanar da shugabancin Akpabio a zauren majalisa wadannda ba su damu da halin da talakawan Nijeriya ke ciki ba.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

 “Abin bakin ciki ne a irin wannan yanayin da Nijeriya ke fama da matsin tattalin arziki a ce shugabannin APC a zauren majalisa suna kin bayyana gaskiya kan zargin almundahanan kan kuaden da za a kawo wa ‘yan Nijeriya sauki a rayuwarsu.”

PDP ta ce Akpabio da ke shugabantar APC a zauren majalisa babu wata barazana ko dakatarwa da zai hana ‘yan adawa fallasa arangizon kudaden al’umma ta hanyar fitar da  sanarwa, rubuce-rubuce a kafaken yada labarai wajen ganin an gudanar da bincike kan zargin yin cushe a kasafin kudi.

Sanarwar ta bayyana cewa jam’iyyar PDP da ‘yan Nijeriya ba sa shakkan shugabannin APC a zauren majalisa, domin wannan cin hanci ne karara a bayyanar jama’a, amma ake kokarin yin rufa-rufa.

Ta ce rashin gudanar da bincike kan zargin cushe a kasafin kudin zai taba kimar majalisar kasa da kuma lalata ayyukan ‘yan majalisa da tsarin mulki da dora musu na gudanar da bincike kan yadda ake kashe kudaden al’umma, sannan kuma ya taba kimar dimokuradiyyar kasar nan idan har aka kasa gudanar da binciken gaggawa.

A cewar PDP, idan har Sanata Akpabio zai yi adalci, to ya gaggauta janye dakatarwar da aka yi wa Sanata Abdul Ningi tare da barin a gudanar da bincike kan arangizon naira tiriliyan 3.7 a cikin kasafin kudin 2024.

Sanarwar ta ce, “Jam’iyyarmu tana aiki kafada da kafada da ‘yan Nijeriya kuma ba za su janye ba har sai Sanata Akpabio ya bari an gudanar da sahihin bincike kan wannan labari da ya zartar da hukunci bisa kuskure.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Aiwatar Da Haramcin Kamun Kifi Na Tsawon Shekaru 10 A Kogin Yangtze

Next Post

Kasar Sin Ta Janyo Jarin Waje Har Dala Biliyan 29.8 A Janairu Da Fabrairun Bana

Related

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

2 days ago
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

2 days ago
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

1 week ago
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

4 weeks ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

1 month ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

1 month ago
Next Post
kasar sin

Kasar Sin Ta Janyo Jarin Waje Har Dala Biliyan 29.8 A Janairu Da Fabrairun Bana

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.