ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Tsugune Ba Ta Kare Ba Kan Zargin Aringizon Kasafin 2024 -PDP

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Zargin

Jam’iyyar PDP ta nunar da cewa har yanzu fa tsugune ba ta kare ba dangane da zargin aringizon kasafin kudin 2024 da Sanata Abduk Ningi ya kwarmata. Inda ta yi kira ga Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sake yin nazari da kuma gudanar da kwakkwaran bincike na gaggawa dangane da kasafin kudin.

Sakataren yada labarai na jam’iyyar na kasa, Debo Ologunagba, ya fitar, da wata sanarwa da ta bayyana cewa PDP tana nan kan bakanta na ganin shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio ya gurfana a hukumar yaki da cin hanci da rashawa domin a bincike shi kan yadda naira biliyan 108 na Jihar Akwa Ibom suka bace da kuma naira biliyan 86 da aka bayar da kwangila ba bisa ka’ida ba a lokacin yana gwamna da kuma ministan kula da bunkasa yankin Neja Delta.

  • Ɗiawara Ya Fice Daga Tawagar Faransa Bayan An Hana ‘Yan Wasa Yin Azumi
  • An Fara Taron Kasa Da Kasa Kan Tsarin Dimokuradiyya Karo Na Uku A Nan Birnin Beijing

Haka kuma jam’iyyar ta caccaki Sanata Akpabio da shugabannin APC kan kawar da hankalin mutane na rashin gudanar da bincike a fili na zaargin cusa naira tiriliyan 3.7 da aka yi a cikin kasafin kudin 2024.

ADVERTISEMENT

“Jam’iyyar PDP ta tabbatar da cewa idan aka tsana bincike za a gano asalin gaskiya game da arangizo a kasafin kudin 2024 da kuma adadin yawan kudaden da aka raba wa ‘yan majalisa na APC,” in ji sanarwar.

Ta kara da cewa wannan lamarin da ya faru ya tabbatar da cewa akwai masu hana ruwa gudu a cikin APC wajen gudanar da shugabancin Akpabio a zauren majalisa wadannda ba su damu da halin da talakawan Nijeriya ke ciki ba.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

 “Abin bakin ciki ne a irin wannan yanayin da Nijeriya ke fama da matsin tattalin arziki a ce shugabannin APC a zauren majalisa suna kin bayyana gaskiya kan zargin almundahanan kan kuaden da za a kawo wa ‘yan Nijeriya sauki a rayuwarsu.”

PDP ta ce Akpabio da ke shugabantar APC a zauren majalisa babu wata barazana ko dakatarwa da zai hana ‘yan adawa fallasa arangizon kudaden al’umma ta hanyar fitar da  sanarwa, rubuce-rubuce a kafaken yada labarai wajen ganin an gudanar da bincike kan zargin yin cushe a kasafin kudi.

Sanarwar ta bayyana cewa jam’iyyar PDP da ‘yan Nijeriya ba sa shakkan shugabannin APC a zauren majalisa, domin wannan cin hanci ne karara a bayyanar jama’a, amma ake kokarin yin rufa-rufa.

Ta ce rashin gudanar da bincike kan zargin cushe a kasafin kudin zai taba kimar majalisar kasa da kuma lalata ayyukan ‘yan majalisa da tsarin mulki da dora musu na gudanar da bincike kan yadda ake kashe kudaden al’umma, sannan kuma ya taba kimar dimokuradiyyar kasar nan idan har aka kasa gudanar da binciken gaggawa.

A cewar PDP, idan har Sanata Akpabio zai yi adalci, to ya gaggauta janye dakatarwar da aka yi wa Sanata Abdul Ningi tare da barin a gudanar da bincike kan arangizon naira tiriliyan 3.7 a cikin kasafin kudin 2024.

Sanarwar ta ce, “Jam’iyyarmu tana aiki kafada da kafada da ‘yan Nijeriya kuma ba za su janye ba har sai Sanata Akpabio ya bari an gudanar da sahihin bincike kan wannan labari da ya zartar da hukunci bisa kuskure.”

Zargin
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Zargin
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
kasar sin

Kasar Sin Ta Janyo Jarin Waje Har Dala Biliyan 29.8 A Janairu Da Fabrairun Bana

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.