ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Tsugune Ba Ta Kare Ba Kan Zargin Aringizon Kasafin 2024 -PDP

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Zargin

Jam’iyyar PDP ta nunar da cewa har yanzu fa tsugune ba ta kare ba dangane da zargin aringizon kasafin kudin 2024 da Sanata Abduk Ningi ya kwarmata. Inda ta yi kira ga Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sake yin nazari da kuma gudanar da kwakkwaran bincike na gaggawa dangane da kasafin kudin.

Sakataren yada labarai na jam’iyyar na kasa, Debo Ologunagba, ya fitar, da wata sanarwa da ta bayyana cewa PDP tana nan kan bakanta na ganin shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio ya gurfana a hukumar yaki da cin hanci da rashawa domin a bincike shi kan yadda naira biliyan 108 na Jihar Akwa Ibom suka bace da kuma naira biliyan 86 da aka bayar da kwangila ba bisa ka’ida ba a lokacin yana gwamna da kuma ministan kula da bunkasa yankin Neja Delta.

  • Ɗiawara Ya Fice Daga Tawagar Faransa Bayan An Hana ‘Yan Wasa Yin Azumi
  • An Fara Taron Kasa Da Kasa Kan Tsarin Dimokuradiyya Karo Na Uku A Nan Birnin Beijing

Haka kuma jam’iyyar ta caccaki Sanata Akpabio da shugabannin APC kan kawar da hankalin mutane na rashin gudanar da bincike a fili na zaargin cusa naira tiriliyan 3.7 da aka yi a cikin kasafin kudin 2024.

ADVERTISEMENT

“Jam’iyyar PDP ta tabbatar da cewa idan aka tsana bincike za a gano asalin gaskiya game da arangizo a kasafin kudin 2024 da kuma adadin yawan kudaden da aka raba wa ‘yan majalisa na APC,” in ji sanarwar.

Ta kara da cewa wannan lamarin da ya faru ya tabbatar da cewa akwai masu hana ruwa gudu a cikin APC wajen gudanar da shugabancin Akpabio a zauren majalisa wadannda ba su damu da halin da talakawan Nijeriya ke ciki ba.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

 “Abin bakin ciki ne a irin wannan yanayin da Nijeriya ke fama da matsin tattalin arziki a ce shugabannin APC a zauren majalisa suna kin bayyana gaskiya kan zargin almundahanan kan kuaden da za a kawo wa ‘yan Nijeriya sauki a rayuwarsu.”

PDP ta ce Akpabio da ke shugabantar APC a zauren majalisa babu wata barazana ko dakatarwa da zai hana ‘yan adawa fallasa arangizon kudaden al’umma ta hanyar fitar da  sanarwa, rubuce-rubuce a kafaken yada labarai wajen ganin an gudanar da bincike kan zargin yin cushe a kasafin kudi.

Sanarwar ta bayyana cewa jam’iyyar PDP da ‘yan Nijeriya ba sa shakkan shugabannin APC a zauren majalisa, domin wannan cin hanci ne karara a bayyanar jama’a, amma ake kokarin yin rufa-rufa.

Ta ce rashin gudanar da bincike kan zargin cushe a kasafin kudin zai taba kimar majalisar kasa da kuma lalata ayyukan ‘yan majalisa da tsarin mulki da dora musu na gudanar da bincike kan yadda ake kashe kudaden al’umma, sannan kuma ya taba kimar dimokuradiyyar kasar nan idan har aka kasa gudanar da binciken gaggawa.

A cewar PDP, idan har Sanata Akpabio zai yi adalci, to ya gaggauta janye dakatarwar da aka yi wa Sanata Abdul Ningi tare da barin a gudanar da bincike kan arangizon naira tiriliyan 3.7 a cikin kasafin kudin 2024.

Sanarwar ta ce, “Jam’iyyarmu tana aiki kafada da kafada da ‘yan Nijeriya kuma ba za su janye ba har sai Sanata Akpabio ya bari an gudanar da sahihin bincike kan wannan labari da ya zartar da hukunci bisa kuskure.”

Zargin
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
kasar sin

Kasar Sin Ta Janyo Jarin Waje Har Dala Biliyan 29.8 A Janairu Da Fabrairun Bana

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.