• English
  • Business News
Thursday, May 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Ta Bankado Sunaye 15 Da Ake Zargi Da Hannu A Tallafa Wa Ta’addanci

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta ce ta bankado sunayen wasu hukumomi 15 da suka hada da mutane tara da wasu kamfanoni shida na Bureau De Change, da ake zargi da hannu wajen ba da kudade a ayyukan ta’addanci.

Sashen Kula Da Harkokin Kudi Na Nijeriya ne ya bayyana cikakken bayanin ci gaban, a cikin wani sakon email da ya aike wa wakilinmu, mai taken “Daidaikun mutane da hukumomi na ranar 18 ga Maris, 2024.”

  • Wuraren Kiwo: Fulani Sun Yi Murna Da Matakin Shugaban Kasa – Ngelzarma
  • Ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa 2 Sun Mutu A Yayin Turmutsutsun Karɓar Abincin Tallafi

Takardar ta bayyana cewa kwamitin takunkuman na Nijeriya ya gana ne a ranar 18 ga Maris, 2024, inda aka ba da shawarar wasu mutane da hukumomi da a kakaba mata takunkumi biyo bayan shigar da suke yi wajen bayar da kudaden ta’addanci.

“Mai Girma Babban Lauyan Tarayya, tare da amincewar shugaban kasa, ya sanya sunayen mutane da hukumomi da za a amfata masu zuwa da aka sanya su a cikin jerin sunayen,” kamar yadda takardar ta karanta a wani bangare.

Daga cikin mutanen da aka bayyana sunayensu a cikin takardar akwai wani mawallafin da ke zaune a Kaduna, Tukur Mamu, wanda a halin yanzu gwamnatin tarayya ke shari’a bisa zargin taimakawa ‘yan ta’addan da suka kai hari kan jirgin Abuja zuwa Kaduna a watan Maris din 2022.

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

A cewar takardar, Mamu “ya shiga harkar tallafa wa ayyukan ta’addanci ta hanyar karba tare da bayar da kudaden fansa kan kudi dalar Amurka 200,000 domin tallafa wa ‘yan ta’addar ISWAP domin sako mutanen da suka yi garkuwa da su a harin jirgin kasa na Abuja zuwa Kaduna.”

Takardar ta ce daya daga cikin mutanen shi ne “wanda ake zargi da kai hari Cocin St. Francis Catholic Church Owo, Jihar Ondo a ranar 5 ga Yuni, 2022 da kuma Gidan Gyara Hali na Kuje, Abuja a ranar 5 ga Yuli, 2022.”

“(a) Ku gaggauta tare da ganowa gami da rufewa, ba tare da sanarwa ba, na duk wasu kudade, kadarori, da duk wasu albarkatun tattalin arziki na mutanen da hukumomin da ke hannunku sannan ku kai rahoto ga kwamitin sanya takuynkumi;

“(b) Kai rahoto ga kwamitin takunkumin duk wata kadara da aka rufe asusunta ko ayyukan da aka yi bisa ka’idojin haramcin.

“(c) Nan da nan ku shigar da Rahoton Mu’amala da ake tuhuma ga NFIU don karin bincike kan ayyukan kudi na irin wannan mutum.

“(d) Bayar da rahoto a matsayin Rahoton Mu’amaloli da ake tuhuma ga NFIU, duk shari’o’in da suka dace da ma’amalar kudi kafin ko bayan samun wannan Jerin sunayen.”

“(a) A rufe duk wasu kudade ko wasu kadarorin da ke hannun mutane da hukumomin da aka kebe, ba wai kawai wadanda ke da alaka da wani aiki, makirci, ko barazanar ta’addanci ko tallafin ta’addanci ba;

“(b) Rufe asusun kudade ko wasu kadarorin da ke da hadin gwiwa wajen mallakarsu ko sarrafawa, kai tsaye ko a kaikaice, ta mutane ko wasu da aka kebe;

“(c) Daskarar ko kuma rufe kudade ko wasu kadarorin da aka samu ko aka samu daga kudade ko wasu kadarorin da aka mallaka ko sarrafa su kai tsaye ko a kaikaice ta wasu mutane ko hukumomi da aka kebe; kuma

“(d) kudade ko wasu kadarorin mutane da hukumomin da ke aiki a madadin, ko kuma a jagorancin mutanen da aka kebe ko kungiyoyi.”

A cewar takardar, Mamu “ya shiga harkar tallafa wa ayyukan ta’addanci ta hanyar karba tare da bayar da kudaden fansa kan kudi Dalar Amurka 200,000 domin tallafa wa ‘yan ta’addar ISWAP domin sako mutanen da suka yi garkuwa da su a harin jirgin kasa na Abuja zuwa Kaduna.”

Wani kuma an bayyana shi a matsayin “dan kungiyar ta’adda ta Ansarul Muslimina Fi Biladissudam, kungiyar da ke da alaka da Al-Kaeda a yankin Magrib.

“An gabatar da batun kuma an yi aiki a karkashin Muktar Belmokhtar, mai lakabi da ‘One Eyed Out’, wanda ya jagoranci Al-Murabtoun Katibat na AKIM a Aljeriya da Mali.”

NFIU ta ce mutumin “ya kware wajen tsara lambar sadarwa ta ‘yan ta’adda kuma shi ma kwararre ne akan sarrafa na’urar fashewa.

“ Bayanin kuma ya ce mai tsaron kofa ne ga shugaban ANSARU, Mohammed Usman aka Khalid Al-Bamawi. Hakazalika, shi masinja ne kuma jagorar tafiya zuwa AKIM Katibat a cikin hamadar Aljeriya da Mali. Yana aikin kafinta.

Batun ya gudu daga cibiyar gyara hali ta Kuje ranar 5 ga Yuli, 2022. A halin yanzu yana kwance a asibiti.”

A wani ci gaban kuma an bayyana shi a matsayin “babban kwamandan Daular Islama ta yammacin Afirka Okene.”

Hukumar ta ce, mutumin “ya fito fili ne a shekarar 2012 a matsayin reshen Arewa ta Tsakiya na Boko Haram.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Takaitaccen Nazari A Kan Yadda Ake Noman Karas A Nijeriya

Next Post

Wasu Daga Cikin Matan Da Ke Sharafi A Nijeriya

Related

Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

4 weeks ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

2 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

2 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

2 months ago
Rikita-rikitar Da Ta Biyo Bayan Mutuwar Mawaki Mohbad
Kotu Da Ɗansanda

MohBad: Nurse Za Ta Fuskanci Shari’a, Sannan Kotu Ta Wanke Naira Marley, Sam Larry Da PrimeBoy

2 months ago
‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja

3 months ago
Next Post
Wasu Daga Cikin Matan Da Ke Sharafi A Nijeriya

Wasu Daga Cikin Matan Da Ke Sharafi A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

May 8, 2025
An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

May 8, 2025
Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

May 8, 2025
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

May 8, 2025
Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar

Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar

May 8, 2025
Zamfara Ta Haɗa Gwiwa Da Oracle A Landan Don Bunƙasa Fasahar Matasa A Jiharta 

Zamfara Ta Haɗa Gwiwa Da Oracle A Landan Don Bunƙasa Fasahar Matasa A Jiharta 

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.