ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Ta Bankado Sunaye 15 Da Ake Zargi Da Hannu A Tallafa Wa Ta’addanci

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Gwamnati

Gwamnatin tarayya ta ce ta bankado sunayen wasu hukumomi 15 da suka hada da mutane tara da wasu kamfanoni shida na Bureau De Change, da ake zargi da hannu wajen ba da kudade a ayyukan ta’addanci.

Sashen Kula Da Harkokin Kudi Na Nijeriya ne ya bayyana cikakken bayanin ci gaban, a cikin wani sakon email da ya aike wa wakilinmu, mai taken “Daidaikun mutane da hukumomi na ranar 18 ga Maris, 2024.”

  • Wuraren Kiwo: Fulani Sun Yi Murna Da Matakin Shugaban Kasa – Ngelzarma
  • Ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa 2 Sun Mutu A Yayin Turmutsutsun Karɓar Abincin Tallafi

Takardar ta bayyana cewa kwamitin takunkuman na Nijeriya ya gana ne a ranar 18 ga Maris, 2024, inda aka ba da shawarar wasu mutane da hukumomi da a kakaba mata takunkumi biyo bayan shigar da suke yi wajen bayar da kudaden ta’addanci.

ADVERTISEMENT

“Mai Girma Babban Lauyan Tarayya, tare da amincewar shugaban kasa, ya sanya sunayen mutane da hukumomi da za a amfata masu zuwa da aka sanya su a cikin jerin sunayen,” kamar yadda takardar ta karanta a wani bangare.

Daga cikin mutanen da aka bayyana sunayensu a cikin takardar akwai wani mawallafin da ke zaune a Kaduna, Tukur Mamu, wanda a halin yanzu gwamnatin tarayya ke shari’a bisa zargin taimakawa ‘yan ta’addan da suka kai hari kan jirgin Abuja zuwa Kaduna a watan Maris din 2022.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

A cewar takardar, Mamu “ya shiga harkar tallafa wa ayyukan ta’addanci ta hanyar karba tare da bayar da kudaden fansa kan kudi dalar Amurka 200,000 domin tallafa wa ‘yan ta’addar ISWAP domin sako mutanen da suka yi garkuwa da su a harin jirgin kasa na Abuja zuwa Kaduna.”

Takardar ta ce daya daga cikin mutanen shi ne “wanda ake zargi da kai hari Cocin St. Francis Catholic Church Owo, Jihar Ondo a ranar 5 ga Yuni, 2022 da kuma Gidan Gyara Hali na Kuje, Abuja a ranar 5 ga Yuli, 2022.”

“(a) Ku gaggauta tare da ganowa gami da rufewa, ba tare da sanarwa ba, na duk wasu kudade, kadarori, da duk wasu albarkatun tattalin arziki na mutanen da hukumomin da ke hannunku sannan ku kai rahoto ga kwamitin sanya takuynkumi;

“(b) Kai rahoto ga kwamitin takunkumin duk wata kadara da aka rufe asusunta ko ayyukan da aka yi bisa ka’idojin haramcin.

“(c) Nan da nan ku shigar da Rahoton Mu’amala da ake tuhuma ga NFIU don karin bincike kan ayyukan kudi na irin wannan mutum.

“(d) Bayar da rahoto a matsayin Rahoton Mu’amaloli da ake tuhuma ga NFIU, duk shari’o’in da suka dace da ma’amalar kudi kafin ko bayan samun wannan Jerin sunayen.”

“(a) A rufe duk wasu kudade ko wasu kadarorin da ke hannun mutane da hukumomin da aka kebe, ba wai kawai wadanda ke da alaka da wani aiki, makirci, ko barazanar ta’addanci ko tallafin ta’addanci ba;

“(b) Rufe asusun kudade ko wasu kadarorin da ke da hadin gwiwa wajen mallakarsu ko sarrafawa, kai tsaye ko a kaikaice, ta mutane ko wasu da aka kebe;

“(c) Daskarar ko kuma rufe kudade ko wasu kadarorin da aka samu ko aka samu daga kudade ko wasu kadarorin da aka mallaka ko sarrafa su kai tsaye ko a kaikaice ta wasu mutane ko hukumomi da aka kebe; kuma

“(d) kudade ko wasu kadarorin mutane da hukumomin da ke aiki a madadin, ko kuma a jagorancin mutanen da aka kebe ko kungiyoyi.”

A cewar takardar, Mamu “ya shiga harkar tallafa wa ayyukan ta’addanci ta hanyar karba tare da bayar da kudaden fansa kan kudi Dalar Amurka 200,000 domin tallafa wa ‘yan ta’addar ISWAP domin sako mutanen da suka yi garkuwa da su a harin jirgin kasa na Abuja zuwa Kaduna.”

Wani kuma an bayyana shi a matsayin “dan kungiyar ta’adda ta Ansarul Muslimina Fi Biladissudam, kungiyar da ke da alaka da Al-Kaeda a yankin Magrib.

“An gabatar da batun kuma an yi aiki a karkashin Muktar Belmokhtar, mai lakabi da ‘One Eyed Out’, wanda ya jagoranci Al-Murabtoun Katibat na AKIM a Aljeriya da Mali.”

NFIU ta ce mutumin “ya kware wajen tsara lambar sadarwa ta ‘yan ta’adda kuma shi ma kwararre ne akan sarrafa na’urar fashewa.

“ Bayanin kuma ya ce mai tsaron kofa ne ga shugaban ANSARU, Mohammed Usman aka Khalid Al-Bamawi. Hakazalika, shi masinja ne kuma jagorar tafiya zuwa AKIM Katibat a cikin hamadar Aljeriya da Mali. Yana aikin kafinta.

Batun ya gudu daga cibiyar gyara hali ta Kuje ranar 5 ga Yuli, 2022. A halin yanzu yana kwance a asibiti.”

A wani ci gaban kuma an bayyana shi a matsayin “babban kwamandan Daular Islama ta yammacin Afirka Okene.”

Hukumar ta ce, mutumin “ya fito fili ne a shekarar 2012 a matsayin reshen Arewa ta Tsakiya na Boko Haram.

Gwamnati
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
Wasu Daga Cikin Matan Da Ke Sharafi A Nijeriya

Wasu Daga Cikin Matan Da Ke Sharafi A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.